Abin da ya sa Buhari ya jinkirta cire tallafin man fetur

Abin da ya sa Buhari ya jinkirta cire tallafin man fetur

 

Abin da ya sa Buhari ya jinkirta cire tallafin man fetur

Mai magana da yawun tsohon shugaban Najeriya, Malam Garba Shehu, ya bayyana cewa tsohon shugaban Muhammadu Buhari ya dakatar da batun cire tallafin man fetur da kuma daidaita tsarin canjin kudin kasashen waje na kasar "zuwa lokacin da ya dace."

Shehu ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin, makwanni hudu bayan da Shugaba Bola Tinubu ya karbi ragamar mulki daga hannun Buhari a ranar 29 ga watan Mayu, ya kuma sanar da cire tallafin man fetur, inda farashi litar mai ta tashi daga naira 184 zuwa sama da naira 500.

Shehu ya kuma yi nuni da cewa idan za a yi “maganar gaskiya a siyasance” gwamnatin Buhari, a kwanakinta na karshe, ba za ta iya ci gaba da aiwatar da gyare-gyaren da ka iya girgiza kasa ba “saboda jami'yyar APC na bukatan lashe zabe”.

''Tun da yanzu zabe ya wuce, shugaba Bola Tinubu ya fi dacewa ya ci gaba daga inda aka tsaya. Mu na da cikakkekn imanin cewa sabuwar gwamnatin za ta sa al’ummar kasa da daukacin al’ummarta su samu kyakkyawar makoma bayan wadannan manyan matakai na tattalin arziki”, in ji Shehu.

Mai magana da yawun tsohon shugaban ya ci gaba da cewa duk da cewa tsohon shugaban kasan bai cire tallafin man fetur ba, amma ya cire tallafin wutar lantarki da tallafin taki da tallafin kan aikin Hajji, da na ziyarar Jerusalem, da tallafin dizal, da na man jirgin sama, da tallafin kalanzir da dai sauransu.

BBC Hausa.

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post