Ƴan sanda sun tarwatsa gungun masu lalata layin dogo a jihar Kaduna

Ƴan sanda sun tarwatsa gungun masu lalata layin dogo a jihar Kaduna

 


Rundunar 'yan anda jihar Kaduna ta bayyan cewa ta bankado wani gugun bata gari da ke lalata layin dogo a yankin Sanzwan da ke garin Zonkwa a karamar hukumar Zango Kataf.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami'in hulda d jama'a na rundunar DSP Mohammed jalige, rundunar ta ce bayan samun sahihan bayanan sirri, jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna a ranar 22 ga watan Yuni, 2023 da misalin karfe goma da rabi na dare, sun yi nasarar fatattakar gungun barayin tare da kama motar da suka zo da ita wacce ke shake da karafunan layin dogo..

Sanarwan ta ƙara da cewa duk da ba a kama waɗanda ake zargin ba rundunar na cigaba da gudanar da bincike kan lamarin.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar ya yaba wa jami’an da suka dakatar da ayyukan ’yan fashin yayin da ya bukaci jama’a da su cigaba da samar da sahihan bayanai a kan lokaci don taimakawa 'yan sanda wurin gudanar da ayyukansu.


Source: BBC HAUSA

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post