Kurkukun Ƙaddara chapter 21 complete


Health College

Kurkukun Ƙaddara chapter 21 complete

 

Kurkukun Ƙaddara

💋KURKUKUN ƘADDARA💋


E21


daga alkalamin Boss Bature, writer of Abban Sojoji🌹


  "Wlh duk wanda ya kuskura ya ƙara ɗauramun alhakin ciwon danish, Sai na yi mashi jahilin Bugun da zai gaza ta shi" A harzuƙe ta yi maganar, nan da nan kowa yasha jinin jikin shi,


  Murya na kerma azeeza tace"dan Allah kowa ya yi haƙuri, nidai bana son tashin hankali, tun da tsohuwa tace mana gobe zai dawo to mu haƙura muje mu kwanta mana"


  Sai da batool ta lalla6a kowannan su kafin ta samu, Suka nufi gadajensu kowa ya haye sama ya kwanta 


Ya rage saura angel kaɗai a tsaye tana  binsu da kallo, Yayin da tunaninta gaba ɗaya yana akan Danish,


   Gyaɗa kai tayi tare da juyawa ta koma saman gadonta, har dare ya tsala bata runtsa ba, Allah na gani ta damu da rashin danish acikin su, tana ji aranta kamar wani abun ne zai faru da shi, ko a wani hali yake a yanzu oho  Allah wa'alamu,


  Lokacin da kowannan su ya yi bacci, tana cikin saƙe saƙe acikin zuciyarta, tajiyo motsin mutun, da sauri ta ƙyalla idonta don taga wanene 


  Wannan mutumin ne me jajayen kaya har ƙasa, hannun shi ruƙe da kaskon turaren wuta, sai yawo yake yi acikin ɗakin su, yana tafiya yana karanto wasu ɗalasimai, hannun shi ɗaya ruƙe da kaskon turaren wutar ɗayan hannun kuma yana amfani da shi wurin kora hayaƙin zuwa kowani sashe na cikin ɗakin,


  Mamaki ne ƙarara akan fuskar angel ga tsoro tana ji, da sauri ta ƙudundune cikin bargonta, ta sanya tafin hannayenta ta toshe hancinta da bakinta kamar yadda ta yi jiya. Aranta tace"Yau ma ya dawo kenan"


   Ya jima acikin ɗakin nasu yana turara masu hayaƙin, kafin taji tsit alamar ya tafi, da sauri ta yaye bargon tana faman sauke ajiyar zuciya, 


  Saukowa ta yi daga saman gadon jikinta na kerma, hasken fitilun nan guda uku ne ya ɗan haskaka Cikin ɗakin, fitila ta ruƙo a hannunta tana haska wurin gadajensu,


  Kamar yadda tabi kowanansu jiya har gadon shi ta tottofe shi da addu'a, haka yau ma tabi gadajen su ta yi masu addu'o'i,


  A daidai bakin gadon danish ta tsaya tana kallon shimfiɗarshi, bakomai ya faɗo mata aranta ba face jiya da tazo yi ma shi addu'a, ya damƙo hannunta yayi tunanin wani mugun abunne take yi mashi, ɗan abunda ya faru jiya atsakaninsu ya tsaya mata arai, matsawa tayi zuwa gefen gadon ta tsugunna tare da leƙa ƙarƙashin gadon tana haskawa da fitila, ganin babu wuƙar anan, yasa tayi tunanin ɗaga katifarshi, 


koda ta ɗaga ƙarƙashin Katifar bata samu wuƙar anan ba, ba ƙaramin takaici taji ba, taso ace Ta gano inda wuƙar take kota samu ta lalata glass ɗin dake ajikin windon toilet ɗinsu,


Allah kaɗai yasan inda ya jefa wuƙar, wata'ƙil ma, ya maida ma tsohowa ita, guntun tsoki taja, yanzu shikenan narasa damar da nake ita? Babu wani makami da zan iya yin amfani dashi wurin rotsa gilashin, kodai naje toilet ɗin In ƙara dubawa? tana yin wannan tunanin ta miƙe da sauri ta nufi Cikin toilet ɗin, Ta tura ƙopar ta shiga daga Ciki, tana haska ko'ina da fitilar hannunta, 


Abu biyu ne Yazo mata aranta, na farko Bokitin da ke acikin toilet ɗinsu Na ƙarfe ne, Na biyu kuma wannan tukunyar fulawar dake ajiye Jikin bango, waswasi ta shiga yi kodai tayi amfani da bokitin? ƙwara shi akan tukunyar fulawar, saboda Zata Iya rugujewa azo kuma buƙata bata biya ba, Anyi asara kenan,


Bata kaiga yanke shawarar dame zata yi amfani ba, ba zato ba tsammani Taji saukar hannun Mutun saman kafadarta, awani irin Firgice tayi kwakkwaran juyi Ta daddage ta ɗaga fitilar hannunta zata kwaɗawa mutun daya dafa kafaɗarta, wani irin ihu batool tasaki a tsorace take faɗin"wayyo! Ke ni ce fa, batool ce,'


 Nauyayoyar ajiyar zuciya angel ta sauke, Tare da janye fitilar, ta daidai ta natsuwarta, ba ƙaramin dariya batool ta bata ba, ganin yadda ta gigice,

  "Allah ya taimake yau, da kin kwanta jinya," 

  Dariya batool tayi"Kin ban tsoro me kike yi acikin toilet ne"? 


    "Ke zan tambaya, dama baki yi bacci ba,? Taya akai kika faɗo mun Cikin toilet batare da neman izni ba, yanzu da ace wani uzirin nake yi fa? 


   Hannu batool ta sanya tana sosa kai, tace"raina ya bani cewa ba abunda kike yi ne, shiyasa na shigo Ciki, Kuma na ganki Ɗazu zuƙunne agaban gadon Danish bansan me kikeyi ba, Amma ina hasashen wuƙar shi kika je nema halan"


  Yatsina fuska angel tayi"I don't know why kin sa mun ido, " ta yi maganar da zolaya,


 Batool tace"saboda na damu dake"

  Ruƙo hannunta angel tayi tare da janta suka fito daga Cikin toilet ɗin, a bakin ƙopar fita daga area ɗin suka ɗan tsaya suna magana,


  "Na duba ko'ina batool banga wuƙar ba, kodai ya maida ma tsohuwa ne?"


 Girgiza kai batool ta yi "I don't think so, nafi tunanin yayi mata wani mugun 6oyan ne, shiyasa na baki shawarar ki shirya dashi, Ku samu kusanci sosai, ta hakanne zaki samu damar sanin inda ya ajiye wuƙar,'


 Tur6une fuska angel tayi"Anya zan samu yardar danish, Kin fa ce yana da wuyar yarda da mutane, balle ni kuma daya ɗaurawa karan tsana,"


 "Ki jaraba ke dai, Danish yana da sauƙin kai sosai, ya danganta da yarda kika tafiyar dashi, amma wani hanzari ba gudu ba, har yau baki faɗa mini me zaki yi da wuƙar Ba!? I ave to know,'

   

 Ta tsareta da ido tana jiran jin amsar da zata bata, ƴan kame kame angel ta shiga yi don batasan batool ta gane ainihin abunda zata aikata, tasan bazata bari ba, zata yi kokarin dakatar da ita ne


Ganin tana ƙoƙarin ƙara tambayarta yasa tayin saurin katse mata hanzarinta da cewa 

"Ko kinsan akwai wani mutumi da ke zuwa ɗakin mu tsakar dare yana yawo da kaskon turaren wuta a hannunshi? 


 Tayi maganar a kokarin ta nata gusar mata da zancen wuƙa,


  "Yaushe kika ganshi"? Angel tace"ko yau yazo, jiya ma na ganshi, idan yazo Sai yaita yin magana cikin wani irin yare mara daɗin ji, sannan yana bin kowani gado yana kora hayaƙin zuwa kowani sashe na ɗakin mu,"


  Maimakon taga mamaki akan fuskar Batool, sai taga ta saki murmushi tare da cewa" kada ki damu kanki angel, tsohuwace ae kullum idan dare ya tsala sai ta shigo ɗakin mu, ta turara mana hayaƙin Kariya,"


 Maimaitawa angel tayi'hayaƙin kariya kuma? Jinjina kai batool tayi eh, mun ta6a tambayarta hayaƙin menene tace mana hayaƙin kariya ne daga sharrin baƙaƙen aljanu domin kuwa akwai su acikin kurkukun nan, kuma hayaƙin yana da waraka acikin shi, shiyasa zaki ga ko ciwo bamu cika yi ba"


  Angel tace"Ni a iya sani na, idan har za'a ba mutun kariya ba hayaƙi yakamata ayi mashi ba, addu'a ya kamata ayi ma shi, sam ni ban yarda cewa hayaƙin kariya bane, dole akwai wani 6oyayyan sirrin a tattare da shi,"


  Kafin batool ta kuma cewa wani abu, suka jiyo sautin shessheƙar kuka daga can cikin ɗakin su,


   "Wanene ke kuka"? Angel ce tayi tambayar tana kallon batool,


Batool tace  "Muje mu duba, ina tunanin Aziza ce, "


 da sauri suka fito daga area ɗin toilet, suka faɗo cikin ɗakin, haskata Angel ta yi da fitilar hannunta, a tsaye suka ganta tsakiyar ɗakin sai kuka take yi tana laluban hanya saboda lalurar da take fama da ita, ta makantar dare (nyctalopia) bata iya gani idan dare yayi, ko kuma idan babu wadataccen haske, haka suke fama da ita, in ta farka zata shiga Cikin toilet, sai ta dinga kuka tana ambaton sunayensu har sai wani ya farka acikinsu ya rakata, 


Tun lokacin da angel tayi noticing lalurar yarinyar, sai da tayi ma batool magana ta tambayeta tun yaushe take fama da ita? Batool ta bata amsa da cewa"tsohuwa tace haka aka halicce ta, da zarar dare yayi ganin ta ya ke ɗauke wa, koda an kunna hasken fitila biji biji take gani" tun daga wannan lokacin angel take jin tsananin tausayinta, tana matuƙar jin yarinyar acikin zuciyarta,  


Ƙarasawa suka yi inda aziza taka a tsaye Angel ta ruƙo hannunta,


   "Its ok stop crying muna atare dake, Ina zaki je ne"?


  Cikin shessheƙar kuka tace"Fitsari nake ji ya matse ni,"


Bari naje na rakata, takai ƙarshen maganar tare da ruƙo hannun azeeza, suka nufi toilet, gefen gado batool ta koma ta zauna tana jiran fitowarsu, badajimawa ba Angel ta fito hannunta ruƙe dana azeeza, har saman gadonta takaita sai da taga ta kwanta, ta janyo mata duvet ɗinta ta lullu6a mata shi saman jikinta, tana jiyo muryar azeeza ta cikin bargon tana faɗin"I luv u so much angel," murmushi angel ta saki tare da cewa"Luv u too my sister, Allah ya kare mun ke, ki amsa da ameen" tana jiyo muryarta tana faɗin"Amen" ba ƙaramin daɗi taji ba, wuce wa tayi zuwa nata gadon ta haye ta zauna tare da jingina bayanta,


"Ba zaki kwanta ki yi bacci ba"? Batool ce ta yi mata tambayar, 


  "Zan kwanta, Ina yin addu'a ne ko baki gani ba" kallonta batool tayi ganin ta ɗaga hannayenta biyu sama tana magana cikin harshen da bata sani ba, da larabci take yin addu'ar,


  "Nima kiyi mun addu'ar, inaso,"

Angel tace"Toh, ki kwanta kiyi bacci, zanyi maki addu'a," amsa mata tayi da toh , kafin ta kwanta,


Bayan angel ta kammala yin addu'ar ta  ta sauko daga saman gadonta, tabi kowani gado ta tottofe su da addu'a, bayan ta kammala ta koma saman nata bed ɗin ta kwanta, 


Daƙyar ta samu bacci ya yi awon gaba da ita, har mafarkin danish sai da ta yi saboda ta sanya wa ranta shi sosai, 


Slowly ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta, dishi dishi ta dinga ganin mutane kewaye da gadonta, sanya cikin baƙaƙen kaya hannunsu zaƙo zaƙo da dogayen akaifu, Kowanne ya ɗaga gudumar dake hannunshi da niyar rotsa mata kanta, A gigice angel ta zabura tana faɗin"Innallallahi wa'inna ilaihirraji'un" sautin dariya taji ta ko'ina acikin kunnanta, hannu tasa ta murza idanuwanta, tare da ware su akan mutanan da take gani, Su batool ne a jere, Sun nannaɗe hannayen rigunansu, Sai faman haki suke yi suna nishi kamar waɗanda suka sha gudu 


"angel tun ɗazu muke jira ki bamu wani training ɗin, duk mun iya wanda kika koya mana" rubina ce tayi maganar,


Nauyayyiyar ajiyar Zuciya angel ta sauke, Ashe idanuwanta badai dai suke nuna mata ba, tayi tunanin wasu shaiɗanun aljanune suka kawo mata ziyara,

 

"Ki tashi Muje mu motsa jikin mu atare" Acewar batool,

 Muryarta a disashe tace"Kun takuramun, ba haka ake ta shin mutun daga bacci ba, duk kun tsoratar dani" taƙarasa maganar tana jifarsu da harara hada murguɗa masu baki, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya, 


Muryar javed taji yana faɗin"Zata taso ko sai munzo mun cuccu6eta"? ya yi maganar yana naɗe hannun rigarshi, ɗaya bayan ɗaya take kallon fuskokinsu, zufa sai tsastsafowa take yi daga jikin su,


Ba ƙaramin burgeta su kayi ba, fuskarta ɗauke da murmushi tace"me yayi zafi javed, yanzu zan taso amma fa saina fara shiga toilet, "


Har suna haɗa baki wurin cewa"To kiyi sauri ki fito, muna jiran ki," ƙarasa janye bargon Jikinta tayi tare da saukowa daga saman gadon, Suka matsa mata hanya tabi ta wuce, 


Walking slowly ta nufi ƙopar shiga makewayinsu, Harta ruƙe handle ɗin ƙopar da niyar ta buɗe sai kuma ta ɗan dakata tare da juyawa tana kallon Haris dake kwance daman gadonshi, idanuwanshi na fuskantar ceilling, da alamun damu atattare dashi, tasan bakomai ya jawo hakan ba, face rashin ɗan uwanshi danish don ta lura ba ƙaramin ƙaunarsa yake yi ba, Yau ce rana ta farka da tafara Jin tausayin haris, duk yabi ya ƙuntata kan shi saboda rashin danish, Allah sarki danish kowa Jikin nashi yake"?


Janye idanuwanta tayi daga kan haris ta mayar dasu kansu Parveen dake a tsastsaye, Tace"Har yanzu ba wani labari game da dawowar danish"?


Jinjina kai su kayi"eh, mu ma munyi expecting ɗin idan muka farka daga bacci zamu same shi kwance a cikin mu, ashe ba'a dawo mana da shi ba"


In brittle voice Azeeza tace"nadamu da rashin ɗan uwanmu, Jiya har mafarkin danish nayi, Allah yasa su dawo mana da shi, idan ba haka ba ni ko abinci bazan Iya ci ba" muryarta tamkar zata fashe da kuka,


Mubeen yace"nikaina daurewa kawai nake yi  amma gaba ɗaya zuciyata a raunace take da rashin danish" yana rufe baki, Naufal yace"idan har jikin danish baiyi sauƙi ba, Zaiyi wuya su dawo mana da shi yau" zuciyarshi a karaye yae maganar,

  

   "Ni abunda nake jima tsoro ma, kada a ƙi dawo mana dashi, kamar yarda ake yi mana  a lokacin baya" Da sauri angel ta kalli fuskar batool da ta yi maganar, a yanayi na jin farga ba, tunawa tayi da tattaunawarsu da ita jiya a cikin toilet area, Inda batool take faɗa mata cewa"A lokacin baya duk wanda aka ɗauko acikinsu ba'a dawo dashi, He has gone forever," da sauri ta shiga girgiza kai tana faɗin"that's impossible, danish must be back, ku kwantar da hankalinku, babu abunda zai same shi, bana so inji kuna xancen cewa ba lallai danish ya dawo cikin mu ba, ' a harzuƙe takai ƙarshen maganar tare da buɗe ƙopar ta shige ciki, Koda ta shiga cikin toilet ɗin a jikin bango ta jingina bayanta, Idonta akan windown nan data kwallafawa ran son fasa ta,


"Da ace xan iya samun damar rotsa gilashin nan, dana yi ƙoƙarin binciko inda treatment room ɗin nan yake, kodan saboda inga danish, bawan Allah, ni tsorona ma kada ya rasa ranshi batare da ya kar6i kalmatusshahada ba, banaso ɗaya daga cikin su ya rasa ranshi batare da na musuluntar da shi ba, idan har hakan ta faru i won't forgive my self, tabbas zanyi asarar jinkirin da nayi,' cikin shessheƙar ku ka tayi maganar tuni hawaye sun soma sintiri akan fuskarta, ta ɗauki tsawn lokaci a tsaye batare da ta ta6uka komai ba, Har sai da tajiyo muryar Batul daga waje tana kwala mata kira"Angel! Angel! Kixo mu yi breakfast giants sun zo, ke kaɗai muke jira" Daƙyar ta iya ɗaga murya tace"Kada ku jira ni, ku fara kawai," 


Takai ƙarshen maganar tare da sanya hannayenta biyu Ta tu6e kayan jikinta asaman igiya ta ɗaura su, wanka ta samu tayi bayan takammmala ta mayar da kayan Jikinta,


Lokacin da ta fito daga Cikin toilet ɗin, A zazzaune ta same su saman red Carpet, a tsakiyarsu wooden trays ne  na kayan abincinsu, kowa ya hallara banda mutun biyu ita da kuma Haris dake kwance yana kallon ceilling, yadda tabarshi haka ta same shi,


Ba irin lallashin da batool ba tayi mashi ba akan ya taso yaci abinci amma ya kafe akan sai an dawo mashi da ɗan uwanshi, a dole suka ƙyale shi,


A hankali angel ta ɗaura idanuwanta akan su giants dake a tsaye kamar gumaka sun goya hannayensu saman ƙirjinsu,


Maimakon taje ta zauna taci abincin, sai gani su kayi ta nufi Inda su giants suke a tsaye, A ruɗe batool ta shiga kiran sunanta tana faɗin"Angel where are u goinig? Ki zo muyi breakfast" ko kallon inda batool take ba tayi ba, Tana ƙarasawa gaban giants, taci burki ta tsaya tana ƙare masu kallo, ga tsoronsu tana ji haka nan ta daure ta cije, ganin kanta take yi wata ƴar ƙaramar halitta agabansu, saboda a Halittar jikinsu, Gabza gabza ne ga ƙirar jiki mai matuƙar razanarwa,


"Pls angel kada kija mana muna zaman lpy, ki dawo ki zauna acikin mu muci abinci" hanna ce tayi maganar,


Yasmin ma tace"Angel, giants basa ji basa gani, Kada ki ce zaki tanka masu, suna iya yi maki illa" Kowa yasha Jinin Jikin shi, duk tana sauraron magiyar da suke Yi mata, amma taƙi koda juyawa ta kalle su, hatta haris dake acan kwance saman gadonshi, Ganin angel agaban giants Yasa shi yin zumbur ya miƙe zaune yana kallon Ikon Allah, Azeeza har ta fara kuka saboda tsabar tsoron kada su cutar da angel,


Sai da angel ta gama kalle su daga ƙasa har sama, Kafin tace"Ko dabba idan a ka yi mata magana tana responding ballanta kuma ku da kuke Jinsin bil'adama,  Meyasa a koda yaushe Kuke yin 6adda kama idan zaku zo wurin mu? Why? u can't even talk to us?  Saboda rashin gaskiya wato kuna tsoron muga fuskokin ku saboda gudun kada mu tona maku asiri nan gaba idan Allah ya ku6utar damu ko? Tayi tambayar cike da tuhuma tana kallon su, Ko motsi wannan ba suyi ba, Balle ma ta gane cewa suna sauraronta,


  "Ko gunki bazai nuna maku yadda ake tsayuwa ba, agoya hannu saman ƙirji, ku dai ga ku nan wasu hamagawa da ku, to kodai ba mutane bane ku? Nafi zargin cewa ku ɗin Robot ne, wato sarrafa ku akeyi daga Can sama, ta yadda baku iya furta komai sai an baku izni koba haka ba"? Tayi tambayar a harzuƙe tana kallonsu,


Su batool sai faman lalla6a angel suke yi akan ta daina yi masu magana tazo suci abinci, amma ƴar tahalikar nan ko kallon inda su ke ba ta yi ba, sai ma cewa tayi"Su rabu da ita, Suci abincin su, Yau sai taga abunda ya turewa buzu naɗi, a tsakanin da giants dole suyi mata magana,

  

   Atsiwace tace"Ba zakuyi mun magana ba? wlh duk ranar da wani ya kuskura acikin ku, Ya furta koda kalmar A ce, zan gano ko wanene shi koda bansan shi ba, idan har naji muryarshi awani wuri zan shaida shi ne, saboda Allah yayi mun baiwar tantance muryar mutane," A zafafe takai karshen maganar, ga yunwa tana ji amma taƙi zuwa taje taci abinci,


Ruƙe qugu tayi"meyasa baku dawo mana da danish ɗin mu ba? ina kuka kai mana ɗan uwan mu? Tsohuwa tace kune kuka zo kuka ɗauke shi"? Tayi maganar tana faman haɗiyar yawu,

 

Aiki fa ya ga angel , ita kaɗai sai sambatu take yi kamar wata zautacciya,


Ganin taƙi zuwa taci abinci Yasa batool taje ƙarƙashin gadonta, ta ɗauko kwandonta, ta kwashe ragowar sauran abincin da suka Ci, da niyar ta ajiye ma angel da haris,


  "Giants we are done," Javed ne ya sanar dasu, yayi hakan ne don su samu su tafi, kafin angel takaiga ƙure su, don in suka fusata, komai zasu iya aikatawa,


Ta gefen angel suka bi suka wuce, Tattara kayan Abincin su kayi a jera suka nufi benan, Ganin zasu tafi basu bata amsar tambayarta ba, yasa ta watsa da gudu ta riga su hayewa saman benen, a jikin ƙofar ta jingina bayanta tare da ware hannyenta, wato ta toshe masu hanyar sa zasu bi su fuce, 


  Tsayawa  su ka yi a tsaye saman matattakalar benan, tunda suke aiki a prison ɗin, basu ta6a ganin hatsabibiyar yarinya irin wannan da take agabansu ba, da ace tasan irin hatsarin dake gare su da bata yi gigin shiga huruminsu ba,


Kallon kallon aka soma Yi atsakaninta angel dasu giants, Hankalin su Batool yayi matuƙar tashi, duk suna a tsaye bakin benan sai roƙon angel su ke yi akan ta matsa ta basu hanya su wuce, ba iri magiyar da basuyi mata ba, amma angel ta maƙe kafaɗa akan bazata matsa ta basu hanya ba, Ita so take taga ikon Allah Shin giants zasu Yi mata magana akan ta basu hanya su wuce ko kuwa"? 

  

Cikin muryar fushi haris Yace"wai ke baki da hankali ne? Ba zaki matsa ki basu wuri su wuce ba? an faɗa maki basa magana, idan ma abunda kike ma hari kenan,"  rai a6ace tace"babu ruwan kowa dani, ku kama harkar gaban......."


bata kai ƙarshen maganar ba, Taga ɗaya daga Cikin giants ɗin ya miƙa ma na gefenshi Kayan abincin dake a hannunshi, Ya kar6a ya haɗa dana hannunshi, Zuba ido tayi tana jira taga me zasu Yi mata, wani irin zazzafan taku giant ɗin yayi yadda kasan Zaki Ya nufi abun harinsa, tuni jikin angel ya soma kerma, ta ƙanƙame jikinta tana girgiza mashi kai, muryarta na kerme ta shiga faɗin"wlh kada ka kuskura ka ta6a....."


(Wannan ne karo na ƙarshe da zanyi posting agrp dinnan, Saboda Baku Comment ba likes, Alamace dake nuna baku so, Don haka meson Cigaban Labri  Yayi mun magna ta whatapp 08103884440) bissalam✍️

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post