AmatulMaleek Page 66 Complete


Health College

AmatulMaleek Page 66 Complete

 

Mamugee

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#



AMATULMALEEK

Mamuhgee

#ZafafaBiyar



66

*MUFEEDA'S FRAGRANCE*

   *GIDAN KAMSHIII* 


Munada kayan turaruka kala kala kama dasu;


Turaran wuta

Turaran jiki

Turaran Kaya

Humra milk

Humra black

Kwalacca

Turaran moping

Freshener

Daidai sauran su 

Ta a Very affordable price.


Zaku iya tuntubar mu a wannan 

07040986690


Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE 


*MUFEEDA'S FRAGRANCE*

   *GIDAN KAMSHIII*



***************

Mummunan halin da Amatu ta shiga ya Sanya anty Farha hadiye nata damuwan maganganun su maamah da mum Aisha dasuka ringa gasa mata masu zafi da 'daci ta janye AmatulMaleek suka fito dakin jiki a sanyaye ta dawo da ita dakinsu.


Suna shiga dakin zaunar da Amatun tayi ita Kuma ta nufi toilet ta shige sbd maganganunsu sun Sosa ranta matiqar gaske musamman mum Aisha datake fadan nata cikin cin zarafi da quntatawa,

Ko Mr Jameel bazata iya kiraba a wannan lokacin sbd itama zuciyarta ta sosu matiqa idan ma ta kirasa bazata iya fadan komai ba kuka ne zaizo mata dan haka ta shige toilet ta rufo kofar batareda ta iya kallan Amatu ba da take nata kukan sosai itama.


Bayan ficewansu mum Aisha kan maamah ta dawo da maganganunta masu quntatawa ta qarasa damawa maamah din lissafi

Husnah kuwa takai matakin da idanuwanta Neman bushewa sukeyi qyam ba hawaye sai ja da radadin zuciya sbd ta kasa yarda da itam ace yau din wai Amatu ce da zuwa dakin Dad dinta da daddare bayan tasan mum dinta ance Koda wasa kar abari tasan da zancen auren bare wannan sabuwar tashin hankalin.

Abin baqin ciki da takaicinta shine yanda Dad dinta duk Isa,kamewa da class dinsa da manyan mata ke bibiya zai iya kallan Amatun ma a mace bare iya taba jikinta,

Babban buri,fata da adduarta shine duk rintsi kada Allah yasa Dad dinta ya Maida Amatu cikakkiyar matarsa,Allah yasa iya wannan da suka Gani ne abin ya tsaya yanda kawai gwara mum dinta ta sani Kila Hakan ne zaisa Dad ya bar Amatun ya dawo da dukkanin rayuwa da kulawansa harma da time dinsa gaba Daya kan mum din nata.


Maamah silalewa tayi zaune tana tare hawayenta sake saukowa kan fuskarta kwata kwata qasar ta fita ranta gaba Daya harma da rayuwa a cikin gidan ASH Dan haka Nigeria kawai take buqatan tattara Amatun su koma ta gaji bazata iyaba,

Zuciyarta bazata iya daukan wannan lamarin ba, bazata iya barin Abeeda ta tasan da maganar auren Nan ba tana guri Daya da ita gwara ta tattara Amatun su koma inda suka fito duk ranar Daya gaji da tafiyar tasu ya warware auren Amma tabbas ta gama zaman gidansa da Amatun.




****Duk wannan tashin hankalin da masifar baisan anayi ba daga shi har Mr Jameel sbd farha ce jinsa da ganinsa a cikin iyalinsa to itama tana cikin sanyin jiki yau din Dan haka wanka tayi ta shirya ta fice daga gidan gaba Daya ta fita kanta ya sake sbd taso fita da Amatun Amma Amatun bazata iya fita koina ba sbd kukan datasha gaba Daya kamanninta sun sauya ga zazzabi ya rufeta na take.


A asibitin kuwa duk wasu formalities na sallama da transfer din Abeedan zuwa Nigeria ta qarasa warware acan sun gama anso Basu nurse da zata ringa kulawa da ita Amma tinda tafiya zasuyi ha zama ba sai aka barta kawai akan zata ringa zuwa kullum nurse din tana dubata kafin tafiyarsu.


A motar ambulance ta asibitin aka kawo Madame Abeedan gida Dan haka suna Jin isowan motar kowannensu ya aro nutsuwar karfi da yaji ya yafawa kansa tareda fuskewa kada ASH ya gano abinda ya faru a gidan ko kadan.


Dayake Shima kusan hankalinsa gaba Daya Yana kan Abeedan da aka kawo gida sai Bai Wani fahimci komai ba hakama little Abeedan Dayaga Bai ganta ba hakama Farha sai yayi tinanin suna tare.


Husnah da maamah farin cikinsu duk da suna cikin dacin zuciya sun bayyana murnar dawowanta a Fili tareda rasa inama zasu ajeta.


Dakunan na qasa a cike suke sbd guda uku ne,

Mum Aisha Daya Se Husnah da maamah Daya sai anty Farha da Amatu Daya.


A sama Kuma bazai yiyuba sbd Hawa da saukan tinda ko motsi Bata iya yi sosai Se ahankali take Dan motsawa daga kallo sai motsi takeyi ko magana Bata iyawa sbd kaman paralyze ne a tattare da ita bayan ciwonta.


A dakin mum Aisha dole aka ajeta nan suka tare sunata dawainiyar murnar dawowanta.



ASH kuwa fita suka sake yi da Mr Jameel sbd so yake ba delay su koma Nigeria tinda Babu abinda zasu zauna suyi din anan Dan haka zai qarasa abinda zaiyi a qasar a ranar sai su Dan huta na kwana biyu kafin su wuce kawai.



Bayan fitarsa kusan yaqe da karfin halin danne ciwon ransu suka ringa yi a gaban madame Abeeda wadda ko Bata komai sunsan tana ji Kuma tana fahimtar komai din.


Wuni guda Amatu Tay a daki kwance cikin zazzabi me qarfi da ciwon damuwa Amma Babu Wanda ya Kalli dakin datake bare dubata sbd kowa a gidan ta ciki na cikinsa.


Anty Farha ma har dare Bata dawo gidan ba Dan haka daqyar Amatu ta iya tashi ta daddafa ta shiga toilet ta sakarwa kanta ruwan zafi sosai tayi wanka.


Dan karfi ta samu da kuzari na wankan datai Dan haka tayi brush ta fito a sanyaye jiki ba kwari ta zauna dole ta daure ta shafa Mai sbd sanyi ta tashi ta saka Riga da wando masu kauri sosai sbd sanyi ta Saka hijab tayi sallolin da suke kanta harma da ishai da lokacinta yayi.


Tana idarwa fitowa tayi Dan dole da yunwar da cikinta ya kasa riqewa kaman zata mutu.


Babu kowa a palon Dan haka Kai tsaye kitchen ta wuce ta Bude fridge ta dauko Coke me sanyi da biscuits ta zauna a kitchen din ta tura hakanan taci sbd bakin da ranta Babu dadi Sam.


Abincin dayake kitchen din ta duba Taga chicken noodles ce Akai duk da Bata Wani so haka ta daure ta zuba a plate ta tura tana ci tana Jin zuciyarta bataso Amma yunwar Bazata barta ba.

Ruwa Tasha me sanyi bayan tagama ta fito.


Husnah data fito daga dakinsu ce ta ganta ko kallan juna basuyiba Amatu ta wuce dakinta Kai tsaye lokacin kusan 10 ta kusa.


Rashin layin kasar yasaka ta rasa yanda zatai ta nema anty Farha Dan haka dole ta kwanta tana shiga damuwan rashin dawowan anty Farha din itama.


Harya kwanta ta manta Bata shigo da ruwa ba dole ta taso ta fito daidai Husnah ta sake fitowa wannan Karan bin Amatun da kallo tayi zuciyarta na tafasa da qunatata da tinanin Amatun dawowan Dad dinta take Jira waton yauma taje dakinsa ta kwana kenan bayan mum dinta tana gidan.


Sauke manhajar Arewa Book domin Cigaba.

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post