kurman Baki page 18 by Huguma

kurman Baki page 18 by Huguma

 *_KURMAN BAƘI_*⚫⚫⚫


*HUGUMA*


PAGE 18

________________________________

https://chat.whatsapp.com/KHGP5vnV6yg6X9CpkQcf39



*_Assalamualaikum warahmatullah_*


*_Kin dade kina neman gurin da zaki siya kaya amintattu masu quality cikin farashi me sauqi?_*


*_ina marabtarku zuwa cikin wannan gida tare da kasancewa da juna,WANNAN GIDANNA HUGUMA CLOSET NA BUDESHI NE SABODA NA BAKU DAMAR SIYAN KAYA MASU KYAU QUALITY DA KUMA SAUQIN KUDI CIKIN AMINCI DAGA GURINA,MASU SIYAN D'AI D'AI DA MASU SARI,NATION WIDE DELIVERY cikin aminci da izinin Allah,Kayan haihuwa na jarirai har zuwa girmansu,ina muna fatan alkhairi ni da ku gaba daya_*

____________________________





            Ita ta fara ankara bayan komai ya kammala,ta tureshi tana sauka a gaggauce daga gadon


"Lokaci yana wucewa fa, za'a kaiwa maman haneefa breakfast" da kallo ya bita yana dan bata rai cikin sigar zolaya


"Shine kuma zaki tureni?" 


"Yi haquri,kai dinne....."ta fadi tana qyalqyale masa da dariya sannan ta tura toilet din ta shige. Har ga Allah batasan abinda yasa yake sake maqale mata ba duk kwanan duniya,abu guda daya ta sani,duk da maganin gyara ingantattu da take hadawa kanta ko da ta siya gurin amintattun da tasan su waye?,zuciyarsu kuma a tsarkake take......bayan wadannan ta naqalci abubuwa masu yawa dake tafi da zuciyar saleem din. Ba ruwanta da abinda ke tafi da zukatan maza,ABINDA KE TAFIYAR DA ZUCIYAR SALEEM ne kawai a gabanta (maza sun banbanta,me yiwuwa abinda ke burge wancan ba shine abinda yake burge mijinki ba,ki karanci mijinki a karan kansa,saiki tsara yadda zaki tafi dashi).


              Yana lalace a gurin yana tuna yadda ruqayyan ke bashi gamsuwa ta kowanne bangare tare da hasaso matsayin Zainab a duk lokaci irin wannan. Zai iya rantsuwa koda ya samu zainab din a matse,amma baya samun nutsuwa da gamsuwar da ruqayya ke bashi. Ruqayya kawai yake kaiwa ziyara ya samu hanyarta ba wani tarkace da zai dinga kawo masa tsaiko,ba dattu da qananun abubuwa bisa hanyar. Ruqayya kadai tasan salon kalaman dake sanyashi yaji ana tsinka masa tunani,kalaman da koda baiyi niyyar kasancewa da ita ba ya dawo babu shiri,kalaman da koda cikin kasuwa yake ta furta masa su zaiji bashi da sauran burin da ya wuce ya dawo gida ya kasance da ita,kalaman da zaijishi tamkar an daukeshi daga duniyar da yake ciki zuwa wata ta daban (sune dirty talk, a hausance ana kiransu da kalaman batsa,Yake budurwa?,kina yiwa saurayinki su koda shi zaki aura?,❌❌❌❌,hakan babban kuskure ne,MIJI shi kadai ake gayawa maganganu na batsa,zaki samu tarin lada me dinmbin yawa,nasan zakice kai?,a batsar za'a samu lada?. Eh tabbas!!!,muddin ga mijin da yake da igiyoyin aurenki ne guda uku,BANCE SAURAYI BA!❌. BANCE WANDA KUKA KUSA KUYI AURE BA!!!❌❌❌. Su wadannan yin wannan maganganun dasu ba abinda yake gadarwa face zallar zunubi da tarun fushin Allah,UWAYEN GIDA DA AMARE KU BIYONI👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽)


(Kowacce zuciya meson bin rudin shaidan ce da kuma son jin gard'in sabon Allah,dukkanmu abinda ke mana waigi ahine tairon Allah tare da tsoron haduwa da fushinsa a ranar gobe. Duk mace ko nakijij da kika basa sabon Allah,bawai don basa so bane,ko don ba zasu iya aikatawa ba,aah.....zallar tairon Allah ne yasa akewa zukata waigi daga aikata hakan. To a wannan zamanin wata fitina ta samemu,Allah S W T ya kawomu wani lalataccen zamanin da wai DIYA MACE BUDURWA DA AKA SANTA DA TSANANIN KUNYA DA KAMEWA, KUNYAR DA HAR AKE SUFFANTA KUNYAR MA'AIKI DA MISALIN KUNYAR BUDURWA saboda sanin tsananin kunya da kamun kai da duk wata 'ya mace budurwa ke da ita. Amma anzo zamanin da yarinya zata iya baje jikinta me tarin daraja tayi hoton tsiraicinta ta turawa wani,anzo zamanin da diya macen da magana ke mata wuya gaban d'a namijin da yake ba muharraminta ba amma yanzu zata iya baje baki suyi magana akan abubuwan da wata matar auren ko zaki saka kanta gabas ba zata iya fadinsu ga mijinta ba!!!. Idan kika ga chart dinsu da ita saikin kisa sumewa. Toke ladingo kina aikin me?,ke baki b'aro zantuka ba ga ladidi can tana ware miki tufka?,me take gaya masa da ke ba zaki murje kunyarki ki gaya masa ba,BAKI AKA FIKI?,KO IYA GAYAWA MIJI BATSA AKA FIKI?.


              Ita zuciya tana da so da kwadayin sabon Allah duk kamewarta,saidai tuna girman Allah da girman azabarsa zai sanya ka dinga tanqwarata kana hanata abinda takeso,ME ZAI SA BA ZAKI TAIMKAKESHI BA?. Idan ma irin wamnan charts din ke burgeshi kuna zaune a falo kowa da wayarsa amma irin charts din kukeyi ke dashi. A bedroom(kuyi haqiri ta kama na gaya muku ne,saboda akwai mata da yawa da idan kikayi magana dasu akan wannan zasuce miki wallahi basusan ma anayi ba,su kunya sukeji da sauransu) irin wadannan kalaman batsan da zaki dinga fitowa baro baro kina gaya masa yana bala'in qarawa musu karsashi da kuzari me azabar yawa,sau da yawa wasu guraren cikin littafi(nawa bansan na wasu ba) zakuji nace ya rada mata wasu kalamai a kunnenta da suka bata kunya/ko ta qunshe kanta/kota gagara tsaiwa/ko ta rada masa wasu kalamai da suka sanyashi sakin murmushi/ko ya qanqameta da sauransu,dukka irin wadan nan kalamanne da bazaiyiwu ka fito ka rubutasu baro baro ba sabanin yadda wasu marubutan ke rubutasun gayansu(muna musu fata da addu'ar Allah ya ganar dasu gudun kada rubutunsu yayi waiwaye bayan dogon zamani ya tadda yara da jikokinsu ya zame musu qaiqayi koma kan masheqiya ya ruguza ginin tarbiyyar da suke gani sun bayar). Kunyar me zakiji ke da suke halal a bakinki tsakaninki da mijinki?,KIN GWAMMACE WATA TAYI MIKI SHUKAR DA BA TATA BA?. Gwara ki tare ko ina,ki tare komai. Da masu farautar sun fara gaya masa zaiga meye sabo a ciki?,ai wance tana gaya min su(kuma bayan kin gama gayan masan kin kunna abinki ga magani a gefe zaki saukeshi,wadancan kuwa idan abun yazo da sauqi basu da abinda zasu saukeshi dashi ta hanyar data dace kaman ke) zaiga meye sabo a ciki?(idan ke zazzafa ce ma kin fisu iya tsara kalaman masu tayar da hankali zaiga bashi da sauran lokacinsu). Mu cire kunya game da mazajenmu ta wannan fannin don Allah,tako wacce siga mu dinga updating muna daidaita kanmu da zamani,KOWANNE NAMIJI DAN DUNIYA NE😂(ba ina nufin duka 'yan iska bane a'ah,amma kowanne namiji yanason rayuwa yana son holewa duk taurin kansa duk miskilancinsa) kada kiga mijinki ustaz ne ko shuru shuru kice ai wane ba ruwansa wallahi KI GWADA KI GANI ZAKISHA MAMAKI MUSAMMAN A OTHER ROOM sanda al'amura suka fara tafiya(DON ALLAH KARKICE KIN TSUFA,KO MISKILI NE wallahi za'a yi babu ke,namiji baya tsufa shikam wallahil azeem,me yasa idan sun auro sa'annin jikokinsu sai kiga sun zama tabararru kuyita zaginsa?😂,tana masa abinda ke kike ganin tsufa yazo ba zaki masa ba,bayan cikin bedroom dinnan daga ke saishi,ba'a taron assembly kuke ba....ku yafemin mommies👏🏽👏🏽😄). Wanda bakinsu haya shuru kuma bance ki bawa kowa labari ba bayan kin gwada,kiyita blushing abinki idan assignment dinki ya samu nasara😄,ki sake fidda wasu hanyoyin kuma a kanki,sai shawara da zaki iya baiwa ga kowacce mace ta tsaftataccen harshe ba tare da kin bankadawa kanki asiri ba. Allah ya dawwamar damu da mazajenmu,wadanda basu da aure ya basu ikon kame kansu ya hadasu da mazaje salihai nagartattu.👏🏽👏🏽



*Ruwan wanka me kyau ta hada ta fara wanka farko. Ta sake hada wani zata sakeyi,har ta dauko sabulunta yau kadai taji qamshinsa baiyi mata ba,ya tsaya mata a hanci da qirji,saita maida ta buda shower gel dinta ta matsa ta fara wanke jikinta. Ita dinma hakanan taji kamar wari wari takeyi mata,amma sai ta kauda kai cikin hanzari taci gaba da wankan tana Allah Allah ta gama.


*********Tana zaune saman gadon asibitin bayanta jingine da bango. Tun a daren jiya kawo yau idanunta da hanakalinta yana kan matar da suka kasance su biyu ne a dakin. Matar da qyar take takawa cikin takatsantsan duk sanda zata shiga bandaki,amma jikinta da bakinta sun nuna ras take,hakanan babu wani me jinyarta koda mutum daya ne,sai wasu nurses guda biyu dake shigowa suyi hira su fice. Yadda suke magana da nurses din yasa ta fahimci kamar qawayenta ne,kuma cikin maganar tasu ta fuskanci kamar dinki aka yiwa matar,saidai kuma dinki wanne iri?,shine abinda hankalinta yafi karkata akai kenan taketa da kwadayin jin dinkin meye akayi mata?.


                 Bata tashi fahimta ba saida nurse din tazo duba dinkin. Mamaki sosai ya kamata,iya saninta masu haihuwa akewa dinki a wannan wajen,to amma ita wannan ai sam bataga alamun ciki ko haihuwa tattare da ita ba. Hasalima batayi mata kama da matan aure ba,tafi mata kama da irin matannan 'yan duniya.


              Bata gushe ba tana ci gaba bin qwwqwafin matar,sai ta lura manyan wayoyi ne a hannunta,hakanan manyan kudade take fiddawa tana kashewa ko a jikinta. 


               Tuni zuciyarta tayi nisa gurin son sanin wace matar?,wanne sirrine a tattare da ita?,tayita Allah Allah hajiyayye ta fita,don ta shirya tunkarar matar qila ta samu wani haske daga gareta.


                Cikin sa'a hajiyayye kuwa ta fita dubiya can ward na yara,da sauri ta sauka a gadon tana daura dankwalinta ta zura slippers dinta ta tunkari gadon.


               Tana kashingide tana danna iphone14 dinta hankali kwance,sai ta daga kai tana amsa sallamar zainab din tana binta da wani kallo.


"Sannu ya jiki?"


"Da sauqi" ta amsa ciki ciki tana ci gaba danna wayarta


"Ni sunana zainab,kuma nice nake jinya a dakinnan" ta fada tana murmushi


"Ayyah sannu" ta sake fada ciki ciki

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post