Cuta ta Ɗau Cuta Page 17


Health College

Cuta ta Ɗau Cuta Page 17

 *_Typing📲_*

   *_CUTA TA ƊAU CUTA_*

             _(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_

_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_

_Shafi na goma sha bakwai

_________

https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr

*_Assalamualaikum warahmatullah_*

*_Kin dade kina neman gurin da zaki siya kaya amintattu masu quality cikin farashi me sauqi?_*


*_ina marabtarku zuwa cikin wannan gida tare da kasancewa da juna,WANNAN GIDANNA HUGUMA CLOSET NA BUDESHI NE SABODA NA BAKU DAMAR SIYAN KAYA MASU KYAU QUALITY DA KUMA SAUQIN KUDI CIKIN AMINCI DAGA GURINA,MASU SIYAN D'AI D'AI DA MASU SARI,NATION WIDE DELIVERY cikin aminci da izinin Allah,Kayan haihuwa na jarirai har zuwa girmansu,ina muna fatan alkhairi ni da ku gaba daya_*

____________________________



........Duk yanda taso daurema zuciyarta haƙurin zuwa safiya ta gagara haka. A haukace ta fice a ɗakin zuwa upstairs da take jiyo hargagin Dafeeq. Yanda take tako steps ɗin da gudu-gudu ya sashi juyowa. Ɗauke kansa yay yana jan wani shegen tsakin takaici, sai dai me, a bazata, matuƙar bazata garesa yaji Khadijah ta wani irin fisgoshi baya har sai da yay taga-taga zai faɗi. Da ƙyar ya iya dafe bango yana bala'in zaro idanun mamakinta.

       “K! Kinada hankali kuwa?”.

    “Banda shi! Ka ɗauka banma san minene shi ba Dafeeq. Amsa kawai nake son ji daga gareka. Shin da gaske ne abinda matarka ta faɗa ko kuwa?”.

   Tsaki ya ja mai ƙarfi yana balla mata hararar takaici. Cikin matuƙar kaifin harshe ya furta, “Amma k jaka ce wlhy. Akan wannan banzar tambayar taki kika min wannan fisgar kamar wani sa'anki ko ɗanki.”

       “An fisgeka ɗin kayi abinda duk zakayi azzalumi macuci. Ka zugani nabar iyayena saboda kai amma ka zagaye kana zuwa wajen naka batare da sani na ba munafuki. Wlhy bazan taɓa yafe maka ba maci amana....”

   Tauuuu!!! Kake jin saukar mari, hannu biyu ta dafe kuncinta wata irin azaba na ratsata. Cikin rufewar ido itama ta ɗaga hannu ta sauke masa lafiyayyen marin tare da watsa masa jajayen idanunta dan Khadijah akwai zuciyar masifa. Tsabar kiɗimewa da mamakinta ya sashi sumar tsaye ya zuba mata ido kawai. Ta nunasa da yatsa jijiyoyin kanta na sake tashi ruɗu-ruɗu. “A da dai ka daka Dafeeq saboda ƙarfin soyayya. Amma a yanzu kaima kasan baka isa ba. Na rantse maka da ALLAH koda zaka kasheni ne da duka sai dai mu mutu tare a wajen ramawa azzalumi. Kai yanzu bakaji kunya ba? Ashe duk abinda kake faɗamin a iya fatar bakinka suka tsaya, na dinga wahalar ɓari a gabanka ashe kaine ke zubarmin da ciki saboda kai jahiline mara ilimi addini. Nayi dana sanin saninka a rayuwata Dafeeq. Nayi dana sanin barin iyayena waɗanda basu taɓa nuna gajiyawarsu a gareni ba tun daga haihuwa har girma saboda kai.....” wani irin kuka mai ƙona zuciya ya sarƙeta. Cigaba tai da nunasa da yatsa tana son yin magana amma hakan ya gagara. 

       Wata shegiyar shaƙa Dafeeq daya gama cika tab da zagin da tai masa ya kawo mata. Kafin tai wani yinƙuri ya buga kanta da bango. Ƙarar azaba ta saki jikinta na rawa, yayinda hannunta ke kan nasa tana kiciniyar ƙwatar kanta amma hakan ya gagara, dan gaba ɗaya haushinta dana Kainaat ne ya tattara a kanta. Yanda yake jin kansan nan har shi wannan yarinyar zataima wannan zagin. Dolene ya nuna mata banbancin mace da namiji. Sai da ya tabbatar ta galabaita da irin shaƙar da yay mata sannan ya shiga jibgarta tamkar an aikosa. Bata da wani ƙarfin koda guduwa, dan tamkar ma numfashinta na barazanar barin gangar jikinta ne. Cikin abinda bai wuce mintuna biyar ba Dafeeq ya jima Khadijah ciwuka tako ina sai jini ke fita gashi ta galabaita ko motsin kirki bata iyayi balle kuka. Ga zagi yana mata na rashin mutunci ta yanda duk wanda ya kallesa yasan yana a cikin matsanancin fushi...


       Headphones ɗin data saka ta cire kunne ɗaya kaɗan dan taji koya haƙura ya tafi, a zabure ta miƙe jin yana dukan abu kamar mutum yana zage-zage. Abinka da dare gaba ɗaya gidan amsawa yake yi. Bama tasan sanda ta zabura zuwa ƙofa ba ta buɗe. “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un ” ta ambata jikinta na rawa idanunta gaba ɗaya a waje. Ganin fa da gaske zai iya kashe yarinyar mutane a gidanta ya ja mata masifa tasa dukan ƙarfinta wajen hankaɗashi gefe da faɗin, “Kai ko kanada hankali yaron nan? Kasheta kake son yi ne?”.

       “Yaro yana bayan uwarsa ke kuma! Idan na kashetan miya shafeki? Ko kinada alaka da ita ne?”. Ya faɗa a zafafe.

    “A'a ALLAH ya rabani haɗa alaƙa da wannan. Kai dai da kaji ka gani kaita kaya. Amma maganar gaskiya bazakai min kisan kai anan ba. Ɗaukarta ku koma inda kuka fito idan ka gadama ma kayi bandarta bai daman ba. A gidana ne dai baza'ai kisan kai ba dan babu mai sakani a masifa ina zamana lafiya.”

         Harara ya zuba mata jikinsa na tsuma, ji yake tamkar itama ya rufeta da dukan ma. Sake watsa mata hararar yay da yarda belt ɗin hannun nasa ya shige ɗakin data fito. Itama hararar ta raka bayansa da ita, kafin ta nufi hanyar ƙasa dan ita kam bataga dalilin da zaisa ta bari su kwanar mata gida ba, musamman ma Khadijah dake nishin mutuwa. Babu jimawa sai gata ta dawo da maigadi. Khadijah dake kwance a sume ta nuna masa. “Kaga ɗauketa ka fitar min da ita a gida, inda ma zaka taimakan ka kaita can bakin titi dan ALLAH tunda ba wani nisa bane”.

     Cike da tsoro maigadi ya ce, “Hajiya bakin titi yanzu a daren nan, idan aka kamani fa? Karki manta mace ce fa wani ma sai ya ɗauka fyaɗe namata ai”.

           “Bamu da wani zaɓi ai Dauri sai wannan. Dan wlhy kaga wannan yarinyar ta mutu a gidan nan kaima bazaka sha ta daɗi ba. Inada dukiyar da zan iya tsallake ƙasar nan batare da ansan ina naje ba. Wannan mahaikacin dana jajiboma kaina wlhy a daren nan zai iya haurewa yabar garin nan shima faɗamin wanene a ruwa?”.

      Rawa jikin Dauri maigadi ya fara, dan tabbas gaskiya Hajiya tafaɗa. Shiko idan hakan ta kasance ai ya shiga uku. Kwata-kwata watansa na biyu kenan da yin aure. Amaryarsa nacan ya baro a ƙauyensu. Kuma Hajiya tasan garinsu koya gudu zata iya saka ƴan sanda su bishi. Ɗaff ya raba Khadijah da ƙasa cikin karkarwar jiki yay sauka zuwa ƙasa. Har cin tuntuɓe yake ga nauyin mutum ko yace gawa dan a yanzu Khadijahn bata da banbanci da hakan. Yana sauka Dafeeq na buɗe ƙofar ya fito, takarda ya jeho batare daya kalla sashen da yabar Khadijah ba. “Karna tashi na ganki a gidan nan da safe. Kije na sakeki saki. Abinda zaki tarar acan ɗin ma ya isheki daga ke har iyayen naki wawuya kawai ƴar iska. Ai ba'a haifi macen da zata maran ta zagan na barta ba, idan kina tunanin kinyi na farko kinci riba yanzu bazaki cita ba kuwa. Dolene kije ki ɗanɗana hukunci mafi tsauri dan nasan rabuwa dani shine mafi girman bala'i a rayuwarki, sai dai ki wuce Legas ki kama ɗaki matsayin karuwa dan waɗan nan iyayen naki masu kama da kafiran farko musamman ubanki ba sake kallonki zai ba”. Daga haka ya koma ciki tare da bugo ƙofar da ƙarfi har sai da Kainaat da ke tsaye galala tana kallonsa da saurarensa ta zabura. Takardar ta ɗauka, cikin matuƙar mamaki ta ware idanunta, dan kuwa da gaske sakin ne har biyu ya rubuta. Ita dake shirin aje mata wajen malami akan hakan sai gashi ta samu cikin sauƙi haka. Kai gaskiya ita ɗin ƴar baiwa she ma to. Wani shegen murmushi ta saki mai ƙayatarwa da sanyaya zuciya, babu tausayi ko ɗar a ranta ta sumbaci takardar da kashe ido ɗaya ta ce, “Kin zama labari a tarihin rayuwar Kainaat Khadijah. Karki damu nima kwanaki biyar ya ragen na biyo bayanki, sai dai banbancina da ke ni wajen mijina masoyina abin alfaharina zan koma”. Dariya ta saki, sai kuma ta dafe bakin da sauri ta sauka ƙasa da gudu. Ta sami Dauri na ƙoƙarin buɗe ƙofar falo zai fita da Khadijah. Cike da nishaɗi ta saƙala takardar a cikin rigar Khadijahn sannan ta buɗema Dauri ƙofar da kanta ranta fes babu tausayi ko ƙanƙani a ranta....


     (Hummm😶).


___________★


       Sosai Anoosh ke laulayin cikin nan. Ga JJ yaƙi zuwa har kwanaki biyu sun wuce. Kullum cikin kiransa Hajiya Lailah tare yana kawo mata uziri. Ganin an tafi sati uku baida alamar zuwa ta fahimci yawo kawai yake da hankalinta. Ranta ya sake kaiwa ƙololiwar ɓacin da ta kasa cigaba da riƙe abinda ke ranta ranar tai masa wankin babban bargo a waya. Tare da tabbatar masa saita wulaƙanta rayuwarsa fiye da yanda ya wulaƙanta mutuncin ɗiyarta. Dan haka ya saurari sammaci.

      Ko tari JJ baiyi a wayar nan ba yayinda Hajiya Lailah ke masifa, sai da ta gama tsaff yaja tsaki kawai tare da kwashewa da dariya ya ce, “Lallai Hajjaju baki san wanene ni ba kenan. Ni kike tunanin wai ki wulaƙanta? To bissmilla ga fili ga mai doki saura sukuwa. Ƴarki kuma da kike maganar na shiga mutuncinta ki tambayeta ai tare muka ji daɗin, hasalima da kanta take kawo min kanta. Dan haka sai ki shirya wulaƙantani da wulaƙantata dan a tafin hannuna take saboda ni bana ƙwaina sai da zakara Hajiya. Ki duba WhatsApp naki ga saƙonan na tura miki, sannan ki shirya taki wulaƙantar ke da ballagazar ƴarki kafin ki shirya wulaƙantanin kinji. Dan na fahimci kin manta duk abinda NAMIJI yayi ado ne, MACE ita ce cikin ruwa tsundum. Na barki lafiya, idan ta haihu namiji a saka masa sunan babanta, idan mace ne kuma Lailah. Kar kuma a haifamin bebiya dan ALLAH hhhahahah”. Ya ƙare maganar da wata irin mahaukaciyar dariya data saka jikin Hajiya Lailah rawa. Gaba ɗaya ma ita ta kiɗime, tsabar yanda komai ke neman juye mata ta rasa ina zata kama. Da ƙyar ta iya kaiwa zaune ta shiga WhatsApp jikinta na rawa. Gigitacciyar ƙara ta saka mai firgitarwa tare da sakin wayar ƙasa ta sulale a sume. Da gudu Anoosh dake kwance a ɗaki cikin bargo ta fito, zubewa tai gaban mahaifiyarta tana mai kwala kiran sunanta da girgizata. Babu alamar numfashi a tattare da ita, baki ta sake buɗewa zata ƙwala kiran sunanta mararta tai wani kalar masifar ƙullewa. Da sauri ta saketa tare da dafe cikin da duka hannayenta biyu. Azaba ta sata kwanciya ta naɗe jikinta waje gudu hawaye masu zafi na tsiyaya a idanunta. Shirun ta ya sata jiyo sautin muryarta daga cikin wayar mahaifiyarta, sauti ne mara daɗin ji da gigitar ta tunani, duk da azabar da take ciki haka takai hannunta dake rawa da ƙyar ta ɗauka wayar, (innalillahi...) Kawai ta iya ambata a zuciyarta wayar na suɓucewa daga hannunta. Ɗaukewar numfashinta dai-dai da ɓallewar jini da ga jikinta tamkar an buɗe fanfo...


       Hajiya Lailah ta fara farfaɗowa gabannin asubahi, yayinda tana buɗe idanunta da ƙyar ta saukesu akan fuskar Anoosh dake kwance hawaye duk sun bushe mata a ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Ƙarnin jini da laimar da taji tana ciki ya sata zabura a firgice. Sai dai da ƙyar ta iya tashi saboda nauyin da kanta yay mata ga jiri na ɗibarta. “Ya ALLAHU Sadiyya!”. Ta kira ainahin sunan Anoosh ɗin da ƙyar jikinta na ɗaukar sabon rawa. Hannu takai da niyyar taɓata sai dai ta kasa, dan ƙirjinta wani irin bugawa yake da sauri-sauri. Yaraf ta koma ta kwanta, dai-dai da shigowar wasu ƙartan maza huɗu cikin falon fuskokinsu a rufe da ƙyalle. Dishi-dishi take iya ganinsu, amma hakan bai hanata ƙarfin halin ambaton, “Su wanene ku?”. Ba

     Ƙyallen ɗaya da ga ciki ya janye daga kan tasa fuskar yana wani kalan taunar cimgam kamar ɗan daudu. Ya kalleta sheƙeƙe yana kaiwa zaune tare da dire kakkaifar wuƙarsa ƙasa yana jujjuyata. Wuƙar Hajiya Lailah ta zubama idanu, sai kawai bugun zuciyarta ya ƙaru. Hannu biyu tasa ta dafe ƙirjinta, sannan ta fara magana da ƙyar. “Na roƙeku idan kashemu kuka zo yi kada ku aikata hakan, idan kuma yazama dole ne, ni ku kasheni ku barmin yarinya ta rayu. Dan ALLAH ku barta ko zamu samu mai mana addu'a ni da mahaifinta. Ita ɗin yarinya ce mai raunin ji da gani, bata san komai ba sai mu da neman ilimi. Na roƙeku kumin hukuncin da duk zaku mata duk da ban san laifin da mukai gareku ba......” tari ne ya sarƙe ta ta kasa cigaba da magana. Maimakon suji tausayinta ma sai suka kama dariya, tare da ɗaukar wayarta suka shiga kallon videon Anoosh da JJ dake cikin wani yanayi, sai dai ba'a ganin fuskar JJ ɗin sai Anoosh. Wani irin ihun shaƙiyanci suka saka daya ƙara ƙarfin bugun zuciyar Hajiya Lailah, a take ta fara aman jini. Sai lokacin sukai kanta, wanda ya buɗe fuskar tasan nan dake tabbatar da ogansu ne ya riƙota ya rungume yana wani abu na ƴan iska da faɗin, “A bari nima na more anan dan naga uwar da ƴar duk jirgi ɗaya ne, ba oga JJ bane kawai zaisha romon nan”.

     Dariya yaran nashi suka shiga yi, babu alamar tausayi a tattare da shi ya bama yaransa umarnin zuwa su bincike gidan duk wani abu mai muhimmanci su kawo masa shi, shi kuma ya shiga aikata sheɗanci da Hajiya Lailah da ita tuni ma ta fita a hayyacinta dan zuciyarta ta buga. Ko a lokacin daya ɗaga daga jikinta da alama rai yayi halinsa ma. Amma babu ko tausayi da imani tattare da shi, da alama ma baisan ta rasuba tsinannen..

       Raba jikinsa da nata dai-dai da dawowar yaransa da tarkace a hannunsu. Na takardu dana wasu abubuwan daban-daban masu alaƙa da dukiya. Sai kuɗi da basu wuce 200k ba da suka samu a gidan. Cikin yaransa wani yaso haikema Anoosh shima amma ganin jinin dake fita a jikinta ya sashi haƙura cike da takaici ya shureta a ciki da shegen takalminsa yana faɗin, “Shegiya ƴar baƙin ciki”. Komai sai da suka tattare har wayoyinsu sannan suka kunna candles guda biyu suka ajiye a kusa da carpet da kujera, basu fita ba har sai da wutar ta fara kama kujerar sannan suka gudu lokacin anata kiran sallar farko ta asubahi.


        Ƙauri da hayaƙin wutane ya fara kai hankalin mutane masu fitowa sallar asubahi. A take aka fara binciken ta ina hayaƙin ke fitowa. Kafin hankali ya kai gidan wuta ta fara ci sosai. Kusan gaba ɗaya rukunin gidajen wajen aka ruɗe. Tuni har mata sun fara fitowa a guje da yara. Kafin kace mi an ɓalle ƙofar gidan da ƙyar aka shiga, tako ina ƙoƙarin kashe wutar akeyi, dan iya falonsu kawai ta kama bata fara zagaye gidan ba. Dalilin wani ma'aikacin ƴan kwana-kwana dake anguwar yasa aka samu nasarar isowarsu da wuri dan shi yay waya. Zuwansu ya bada gudunmawar samun nasarar kashe wutar akan lokaci, yayinda aka fito da Anoosh da Hajiya Lailah jikinsu duka a saɓule ko iya shaidasu ba'ayi. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Wannan tashin hankaline da ba'a taɓa ganin makamancinsa ba a anguwar, an wuce dasu asibiti duk da ba'a da tabbacin ma suna numfashi. Yayinda mutanen anguwa keta faman kuke-kuke. Dan Hajiya Lailah mutuniyar kirki ce, sannan Anoosh yarinyace mai tarin nutsuwa da hankali, sannan a dunƙule ma rayuwarta abar tausayice ga duk mai imani kasancewarta bebiya ga raunin gani, ga rauni na kasancewarta ɗiya mace. Kai koda maƙiyinsu a yau hankalinsa tashe yake. Gashi babu wanda yasan danginsu sai Gwaggo kuma itama ALLAH yay mata rasuwa. Sai kuma wanda kowa yasan Anoosh zata aura wato JJ. Dan haka ma wanda suka ɗan sanshi musamman waɗanda Hajiya Lailah ta wakilta suka amshi kuɗin auren Anoosh hankali tashe suka nemosa a waya, tare da faɗa masa ya maza yazo su Hajiya Lailah sunyi gobara.........✍️


_Nagode da addu'oin ku tare da kiran wayoyinku🙏🏻🙏🏻😘😘😘_

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post