Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe Page 7 complete


Health College

Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe Page 7 complete

_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_

سجن القدر💋✊🔥

~Takun Ƙarshe🔥~

قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘

An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘

Daga alƙalamin Boss Bature💋✊

__________________________✍️

 Tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace"Ina da banbanci dasu, Har Yau har gobe sunƙi mantawa da matsayina a gidan ku, Suna yi min kallon ƙasƙantacciya Ƴar aiki, babu abunda Ya canza" 


  Ya fahimci baƙaramin jin shakkarsu ta ke yi ba, muryarshi a kausashe ya furta"kamar ba matar Sir mubarak ba, kin bani  kunya, wlh daga yau zan baki last warning, idan na kuskura na sake ganin kin zubda hawayen ki ko kina jin tsoron wani acikin su, sai na sa6a maki" ƙiris ya rage ta fashe mashi da kuka, jin yadda yake mata magana da faɗa.

 Zare mata ido yayi"ina fata kin fahimce ni"? Muryarta na rawa furta"yea..h" ruƙo hannunta yayi acikin nashi, yaja ta a hankali suka nufi katafaren falon gidan, ko da su ka shiga masu yi masu hidima suka taras sai kai komo su ke yi a cikin falon, ganin sir mubarak yasa suka yi saurin gaishe su cikin girmamawa bayan ya amsa masu ya tambayi ina gimbiya mujeedat.


 Ɗaya daga cikin hadiman ce ta bashi amsa da cewa"su na a garden"


 Damƙa mata hannun Turai yayi wadda tuni jikin ta yayi sanyi lakwas.


 Cikin kuwala yace da hadimar "she's my wife, inaso ki rakata wurin su, ki bi min ita a hankali' murmushi hadimar tayi aranta ba karamin burgeta yayi ba, daga gani yana daraja matarshi

  "In sha Allah yalla6ai" ta faɗa tare da ruƙo hannun mom Turai suka nufi ƙofar fita daga falon, tana tafiya tana waiwayon shi, kamar yadda shima yake kallon ta har sai da ta 6ace ma ganin shi kafin ya nufi ɗakin prime minister.


Jin motsin shugowar Sir Mubarak ne Yasa shi Buɗe idanunsa Yana dubanshi

  Daga gefen gadon shi Ya zauna Yana fadin"ƙanina Ya Gajiyar tafiya," miƙewa Hateem Yayi da wata irin kasala Ya zauna Yana fuskantar Sir mubarak

  "Gajiya tabi Jiki, yayana nakaina, kaima ya gajiyar taka"

 Da zolaya Sir mubarak Yace"nifa Sojane tafiyar da mukayi bata isa ta gajiyar dani ba" murmushi Hateem Ya sakar mashi

Cikin kulawa Sir mubarak Yace"Meke damunka? Naga yanayinka ya canza ko baka Jin dadine"?

  Cikin sanyin Murya Yace"lafiyana lou" ya fada yana kokarin danne damuwarshi

 "Nifa Yayanka ne Hateem, baka Isa ka 6oye min damuwarka ba, dan Allah ka faɗamin, Idan ba haka ba hankalina bazai kwanta ba, na fahimci tun da kazo ƙasar nan ka canza gaba daya"

  Ruƙo hannun sir mubarak Yayi acikin nashi ya damƙe shi sosai.

    Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta"bansan ya zanyi ba da ƙaunar yaron nan na wurin Owais, shine silar duk wani hali da nake aciki, Har mafarkin shi nake Yi" ya faɗa yana mai sanyaya muryarsa.


"Allah Ya jarabce ni da son shi, bani da alaƙa da shi amma sai nake jin kamar ni na haife sa, na faɗa maka ne saboda kana ɗaya daga cikin waɗanda suke fahimtana"


  Tun da ya fara magana Sir mubarak yake binshi da kallo mai nuni da tausayawarsa gare shi, yasan bakomai ke damun shi ba face rashin samun ɗa namiji, shiyasa ya kwallafa rai akan yaron da owais ke ruƙo.


  "Ban ta6a ganin shi ba, amma saboda kai In sha Allah zanje har gidan owais ɗin In ga Yaron zuwa Gobe In Allah Yakaimu"


  "Yana kama dani, tamkar Anyi photocopy din fuskana, hasken fatane kaɗai Ya banbanta mu da shi, Fatarshi farace Sol, tamkar Nazli, Dalilin dayasa kaga nashiga halin nan, bana son inbar ƙasar nan batare da yaji saukin lalurar shi ba, ina matuƙar son mu gana dashi, sai dai na rasa wannan damar da nake da ita, baba ya hanani kusantar shi, Gidan Owais dinma An hanani zuwa saboda shi, dole In hakura" cikin karyayyar murya ya faɗa yana faman sauke numfashi.


   Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, yana neman rudar dashi, Aranshi Ya ayyana wannan wata irin kaunace haka? Abu kamar aikin asiri Allah na tuba.


 Lallashin shi ya somayi yana kwantar mashi da hankalin shi, Har saida Yaga yafara sakewa tukunna suka cigaba da  tattaunawa a tsakanin su.


__________________✍️


Lokacin Da Hajiya Turai, Ta shigo garden din tare da Hadimar data rakota, Tunkafin Ta ƙarasa inda su Gimbiya mujeedat suke, Hajiya laurat ta rafka salati tana fadin"wa nake gani kamar Harriet ƴar aikin gidan baba obie" ta kira ta ne da ainihin sunan ta, gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta, Hadimar data rakota Harta Juya ta nufi hanyar komawa gidan, Jiki asanyaye turai take tafiya tana tunkarar su.


 Wani irin Matsiyacin kallo Hajiya laurat da Hajiya saratu suke watsa mata.


   Tuni tasha jinin jikinta, da hannu Hajiya laurat ta nunata"ke! meya kawo ki nan? Ko kinga sa'ar Yin ki ne"


   Shiru tayi bata tanka mata ba, Hajiya saratu ta kwashe da dariya Tana fadin"shisshigine da kutsu irin na ɗan talaka, malama wani tsautsayinne ya kawo ki wurinmu? Ko aiko ki akayi don ki yi mana hidima ne"?


  Cike da shaƙiyanci her excellency Muhibbat tace"jibarta kamar wata mutuniyar kirki, ita kanta ta raina kanta shiyasa take jin shakkar shiga cikin mu, Ni wlh bansan me mubarak Ya gani a jikinta da har Ya aureta ba, in banda hasken fatarta da gashin da take da shi, Mace kullum kamar ana ɗibar namanta ana miya da shi, babu ƙiba babu tsawo, Duk arziƙin da take ci," Dariya suka sanya, mutun ukune basu tanka mata ba, Gimbiya mujeedat da hajiya malikat sai Hajiya madina. Sauran sune hatsabiban.

   Hajiya Jamila tace"ai auran nata da yayi bana Allah da annabi bane wama yasani kota asirce shine, saboda Sir mubarak yafi ƙarfinta nesa ba kusa ba, Babban gorone, Shiyasa ta nace mashi don aci arziƙi, don Ma Allah Yasa bata ta6a haihuwa da shi ba, sai dai taci ta zubda....  " Hankalin turai ba ƙaramin tashi yayi ba, Jin cin mutuncin da suke Yi mata, Tuni hawaye sun soma wanke fuskarta.

  Hakan ba ƙaramin daɗi yayima hajiya laurat ba, Ita dama burinta takala Ya ƙuntata.


 "Nifa Har yanzu ban daina zargin Yaron nan nata shege bane, tun da bashi da uba, ahaka tazo da shi aiki gidanmu daga ƙasar england, matar nan muguwar munafuka ce, babu Allah aranta, Allah kadai Yasan maƙarƙashiyar da take kulla mana" zaro ido waje Hajiya turai tayi jin abunda Saratu take fadi, Maganar ta ƙona mata ranta, zuciyarta har wani tafarfasa take Yi sam takasa buɗe baki ta dakatar da su, sai dai binsu da take Yi da idanu.


   "Gobe kada in kuskura Inga ƙeyarki awurin taron shagalin dinner din da za'ayi na Hateem, Idan ba haka ba agaban idon kowa zan watsa maki ruwan lemu akan fuskarki" Hajiya laurat ce ta fada tana nuna ta da cup din hannunta.


  "Dake da wannan ɗayar munafukan meye ma sunanta"? Da sauri hajiya saratu tace"hajjaty" hajiya laurat tace"yawwa ita nake nufi, uwar iyayi, mai shafa turaren ƴan bori, ku biyun nan bamu buƙatarku a family din nan don kawai ba yadda zamuyi daku ne amma very soon zamu yi maku korar kare" ta faɗa tana sakar mata shu'umin murmushi.


 Fashewa Turai tayi da kuka mai cin rai, kamar an ruƙe mata ƙafafuwanta takasa tafiya tabar wurin su.


Gyaran murya Gimbiya Malikat tayi masu, gaba ɗaya suka kalleta.


  "Ba girmanku bane, kun bani Kunya, ni banga amfanin maganar da kuke gaya mata ba, ku kama mutunci ku mana" rai 6ace ta furta maganar, babu wasa a fuskarta.


  Sai lokacin Gimbiya Mujeedat ta buɗe baki cikin nutsastsiyar muryarta ta furta Sunan turai.


Baiwar Allah muryarta na rawa ta amsa mata da na'am.


  "Zo ki zauna kusa dani" ta fada tana nuna mata gefenta.


  rai a6ace Laurat da muhibbat suka miƙe tsaye suna fadin Allah Ya kiyaye su haɗa kafada da ita, Indai turai zata zauna sai dai su su tafi" ko kallon su mujeedat batayi ba.

  Muryar turai da shessheƙar kuka tace"bazan Iya zama ba Aunty mujeedat, bana so na shiga tsakaninku, ni zan tafi kawai, dama yaya mubarak ne Yace in zo wurinki don inyi maki bangajiyar tafiyar da ku ka yi, don haka zan tafi tun da naganki..... " tana ƙarasa maganar, ta juyawa da sauri ta nufi hanyar fita daga garden din.


  Zuciyar Gimbiya mujeedat ta sosu, ranta ya 6aci da kalaman da Su laurat sukayi ma Turai.

   Yunƙurawa tayi tare da miƙewa tsaye tana gyara rigarta,

  Har suna hada baki wurin tambayarta ina zataje?

 Batare da dube su ba tace"zan shiga cikine, nagode da ziyara sai mun haɗu gobe idan Allah yakaimu" Ta fada tare da kallon Gimbiya malikat tace"mu shiga daga ciki," miƙewa hajiya malika tayi suka ruƙe hannun juna atare suka nufi cikin gidan.


Bayan tafiyar su, Tsoki Hajiya laurat taja tana fadin"wannan munafukar matar duk itace taja mana, Muna zaman mu lafiya, ta tarwatsa mana farin cikin mu"

Hajiya Jamila tace"Halin talakan kenan,  Yanzu gashi tasa Ran gimbiya mujeedat Ya 6aci"

 Hajiya saratu tace"banji dadi ba wallahi, amma nasan ta inda zan rama, Allah yakaimu gobe lafiya, Idan har matarcan ta kuskura ta zo dinner din ya hateem jikinta zai gaya mata sai nayi mata abun da bata ta6a tsammani ba" ta faɗa tana faman haɗe fuskarta, Sun jima a garden din kafin daga bisani kowaccensu ta shiga motarta suka nufi gidajensu.


Baiwar Allah Hajiya turai tana azaune cikin motar Sir mubarak, tasha kuka tamkar ranta zai fita tayi danasanin zuwa gidan prime minister, kalaman su sun ƙona mata rai, musamman da hajiya saratu ta ambaci jazz da sunan shegene, tayi alkawarin bazata fadama sir mubarak abunda suka gaya mata ba, don kuwa idan yaji sai sun yabama aya zakinta.


_______________________✍️


Baka jin sautin komai a falon tamkar babu mutane acikinsa, alhalin nan kuwa Suna zaune kowa Ya hakimce abun sa, tsabar miskilanci ne Yasa basa iya buɗe baki su tanka ma Junan su, Kowannan su da abunda Ya ɗauke mashi hankali, fitowa Dr jazz yayi daga bedroom dinsa ya kimtsa kanshi cikin shadda launin blue sky abunka ga farar fata ta ƙara fiddo mashi da hasken shi, ga wani daddaɗan ƙamshin turarensa dake fesowa, Ya gyara sumar kanshi hannun shi ɗaya ruƙe da key din motarsa, wani irin annurin farin cikine akan kyakkyawar fuskarshi ga dukkan alamu akwai wani abu daya faranta mashi rai.  


kafin Ya ƙarasa cikin falon, Idanunsa suka hango ma sa Matasan Samarin Family din dake zaune saman sofas Har sai da gabanshi Ya faɗi da idanunsa suka yi mashi tozali da su, Baisan da zuwansu ba, aranshi ya ayyana to fa ashe yau muna da manyan baƙi a gidan na mu ba, meyasa Ibad bai faɗa min sunzo gidan nan ba? Ya ƙarasa zancen zucin nashi cike da jin fagabar tunkararsu, Ya kasa motsa ƙafafuwanshi Ya tsaya atsaye kamar wanda aka yi mashi Iyaka da shiga falon, ɗaya bayan ɗaya ya soma bin su da kallo, Zaki Yana a azaune saman 2 seater Yayin da Apple Laptop dinsa ke akan Table din gabansa, Gaba ɗaya ya tattara hankalin shi akanta yayin da yake operating dinta atsanake, Short ne a jikin shi tare da Denim shirt tabi shape dinsa, Kau da idanunsa yai daga kan Zaki Ya mayar da su kan Wani Matashin saurayi fari Sol, fatarshi ko ƙwarzane babu, Ga wata nannaɗaɗɗiyar sumar kai dark brown, kai daga ganinsa wani shege ne mai ji da naira, Allah yayi shi da kyau mai jan Hankali, Jallabiya ce a jikin shi launin grey, ta zauna mashi sosai, bakowa bane wannan face Captain YASEER ɗan gidan His Excellency Abdul Razak da Her Excellency Muhibbat shuwa arab ne kamannin shi sak dana su Chief Owais, banbancin su launin fatane dana Ido, hannun shi ruƙe da Expensive phone dinsa da yake daddanawa da zira ziran yatsun hannunsa, yayin da Justice Nadeem ɗan gidan His excellency Deen Yake a kishingide kan doguwar Sofa, Ya zagayo da hannun shi ɗaya saman forehead dinsa, idanunsa suna a lumshe tamkar mai yin bacci.


Ziyad ne kaɗai yake a zaune saman lallausan Carpet din dake a shimfiɗe tsakiyar Sofa set din falon, faffaɗan farantin da aka kawo masu fresh fruit acikinsa ya tasa a gaba yana shan kayan marmari, duk acikin su Ziyad yafi su sauƙin kai kasancewarshi ɗan jarida da son labari, A yanzu haka da yake a zaune cikinsu A takure yake jin kanshi sunƙi sakar mashi fuska su yi fira kowa Ya kama harkar gabanshi shiyasa ya sauko kan carpet yaci gaba da shan kayan marmari.


Ƙamshin turarensu Ya gauraye Falon, Jazz dake kallon su ba ƙaramin burge shi su ke yi ba, ba tun yau ba Yana son Yaga jikokin Baba Obie sun haɗu suna sada zumunci aranshi sai yaji inama ace shima Jikan Baba obie ne da Allah ne kaɗai Yasan irin Farin cikin da zaiyi a duniyar nan.


Ganin basu lura da shigowarshi falon bane yasa shi yin saurin tafiya cikin sanɗa Ya nufi ƙofa Ya fuce daga ciki Yana faman sauke ajiyar zuciya, da sauri Ya nufi Harabar Ajiye motocinsu, Ya buɗe motarshi Ya shiga daga Ciki, tare dayi mata key, zuciyarshi acike fal da tunaninta, fatan shi Allah yasa wannan karan ta kula shi.

  Yana driving fuskarshi dauke da annurin farin ciki, A haka Ya nufi Gidan baba obie.


Ganin shirun nasu bamai ƙarewa bane, Yasa shi miƙewa, Ya nufi Zaki Ya sanya hannu ya ɗauke laptop din da yake dannawa, Ya juya Ya nufi Captain Yaseer Ya kar6e wayarshi, kafin Ya tunkari justice Nadeem Ya sanya hannu Ya kamo Hancinshi Yaja Shi da karfi har sai da Justice Nadeem Ya buɗe idanunshi dake dauke da bacci Fuskarshi adaure yake kallon Ziyad.


 Harara Ziyad Ya watsa masu Ranshi a6ace yace"wai meke damunku ne? Kullum muka haɗu kamar wasu kurame babu mai magana kowa ya kama harkar gabansa? Haka ake zumunci? Ni banga amfanin kirana wurin nan donmu haɗu ba.... " gaba ɗaya sun ɗaura idanunsu kan fuskarshi babu alamun zasu tanka mashi.


  Guntun tsoki Yaja"kun wani zuba mun idanu kuna kallona wato ni ga shashasha"

Yamutsa fuska Zaki yayi tare da miƙa mashi hannu yace"Bani laptop dina ziyad"

 "Ta ƙarfi ce zoka kwata" A faɗace Ya faɗa Yana haɗe mashi fuska.


 Murmushi gefen fuska Zaki Ya sakar mashi.


 "Meye damuwarka"? Ya tambaya yana faman lumshe idanunsa.


   "Damuwata shine ku bani aron hankalin ku muyi fira kan abunda ya shafi rayuwarmu, daga gobe fa shikenan kowannanku zai koma inda Yake rayuwarsa, yawanci ba akasar nan kuke zaune ba why ba zamu kula juna yadda ya dace ba? Bamu da tabbacin ko zamu sake haduwa da junanmu"


  Yanayin yadda yayi masu maganar Ya ta6a zuciyoyinsu, 


  In a calm voice Zaki Ya furta"In sha Allah zamu sake haɗuwa, Yanzu dai ka yi haƙuri, Ka zauna mu yi fira"


  Ta6e baki Ziyad yayi, kafin Ya koma Ya zauna, Batare daya miƙa masu Kayansu daya kar6a ba.


     "Bro, Ni bansan ta yadda zan fara firar bane, ko zaka taimaka mana da abun da zamu tattauna akai"? Captain ne Ya faɗa Tamkar baison furta maganar, justice Nadeem dake a kishingiɗe tuni Ya gyara zama saman Sofa Yana duban su

    

     "Me zai hana Mu yi magana dangane da matayen da muke da burin aure"? Acewar ziyad.


 kallon Harara Captain Ya watsa mashi"mu yi magana kan abu mai mahimmanci, Idan ba haka ba zan ja baki na nayi shiru"! 


  "Aure shi yafi komai mahimmanci domin kuwa Sunna ce mai karfi ta Manzon Allah SAW, Allah Ya bamu komai da zamu buƙata, Kowannanmu Yana da aikin yi, Aure shi ya rage mana yakamata ku yi tunani yanzu fa lokaci ne da zamu more rayuwarmu, mu ma yi aure mu hayayyafa kamar yadda Iyayen mu suka yi.... " Ziyad ne ya kora masu jawabi.


  "Look, Ni aure baya a gabana yanzu, har yau banga macen data kwanta min arai na ba, tun lokacin dana rasa wadda nake da burin aure naji matan ma sun fitarmin araina"


  Justice Nadeem dake kallon Captain Ya saki murmushi tare da cewa"Ai ba ita kadai bace mace a family dinmu ba, Kai ma kaso ka wahalar da kanka, Ai ni tun lokacin dana fahimci macace mai izza da ji da kai, na sanyama zuciyata salama, saboda bana son macen da namiji bai isa yayi iko da ita ba, ba zata yi dadin zaman aure ba, kwara wadda zaka Iya juyawa son ranka ba wadda zaka dinga jin fargaban tunkararta ba"


  Ziyad yace"ka faɗi gaskiya mutumina,  ita fa gaba ɗaya namiji ma baya agabanta, bata da burin yin aure, kai ma mai yaja maka yin dakon soyayyarta? Bayan Ga matasan ƴan mata nan masu jini a jika a family namu.... " kafin Ziyad ya ƙare maganar, Zaki yai gyaran murya tare da cewa"wai kuna Nufin Nazli"? Ɗaga mashi gira Nadeem yai, matashin murmushi ya saki kafin yace"Kuna nufin bakusan alaƙar dake a tsakaninta da chief Owais namu ba"? Atare suka haɗa baki wurin furta meke nan"?


   Jim ya ɗanyi kafin Ya furta"Uncle Hateem, Ya riga daya mallaka mashi ita, bata da wani miji daya wuce shi a duniyar nan, tun kafin tazo duniya, wannan alƙawarine dake atsakanin Uncle sharafudeen da uncle Hateem, zasu haɗa auran ƴa'ƴansu... " da mamaki suke kallon shi

  Ziyad yace"amma ni banta6a ganin alamun suna kula junansu da sunan soyayya ba, Ko ranar Birthday din grandfa da suka haɗu ko kallo ba su wa junansu ba"

 "Dama taya za'ai su kula juna?bayan kowannansu Yana ji da kanshi daga ita har shi Owais din, duk abunda take taƙama da shi shima Yana da shi, gaskiya Uncle sharafudeen da Hateem basu yi tunani mai kyau ba, bayan sanin cewa Izza A jinin su take, tayaya Nazli zata yi mashi biyayya amatsayin matarshi? Justice Nadeem ne yayi maganar.


 Captain da ke sauraransa fuskarshi babu annuri babu walwala ya furta"da ace nasan da zancen nan da tuntuni na cireta araina, dama ni ba Iyawa zanyi da ita ba, owais din shi yafi dacewa da ita, suje can su ƙarata," Ya faɗa tare da jingine kanshi jikin Sofa.


      Shiru suka yi na ɗan wani lokaci, babu wanda Ya furta magana sai daga bisani Justice nadeem Ya furta"Zaki Ina budurwarka ta Canada Kyakkyawar balarabiyar nan"


 Da zolaya ya faɗa yana duban shi.

 Kallo ya jefa mashi mai kama da harara kafin Ya furta"ta koma gidan su"

 Zaro ido justice Nadeem yayi"me? Kana nufin tabar gidanka"

 Ɗaga mashi gira yai alamar eh,

 "But why"?

Bai cika son tada maganarta ba, saboda hakan Yana fama mashi raunin dake a zuciyarshi.

  Cikin sanyin murya ya furta"bansan meyasa ba, rana ɗaya ta haukace min ta soma kokarin juya min ba, badan naso ba nabarta ta dawo Nigeria"

     Justice Yace"banji dadi ba, me zai hana ka nemi gidansu inyaso saika gabatar da kanka wurin Iyayenta"?

  Murmushin takaicin Zaki yayi"tana da aure har da ƴarta, ban ta6a fada maka bane"

   Jin wannan maganar Yasa Captain ware manyan idanunshi, hatta Ziyad dake sauraransu saida Ya zaro ido da alamun mamakin kalaman Zaki

  A ruɗe justice Nadeem ya maimaita maganarshi"tana da aure har da ƴa? Amma ta zauna a gidanka tsawon shekaru tamkar ma'aurata? Kafin Ya ƙare maganar Captain Yace"tayaya hakan zai yiwu? Nima fa nasan Matar duk lokacin da zanje canada a gidan ka nake taras da ita, nayi tsammanin Ƴar aikin ka ce, shiyasa ban ta6a kawo ma raina wani abu ba," 


   Girgiza kai Zaki yayi"ba ƴar aikina bace, Taimakon ta nayi, na ruƙe ta agidana saboda ta nuna min bata da kowa bayan mun fara shaƙuwa take bani labarinta, Hankalina Ya tashi jin cewa tana da aure, amma agidana mijinta ya tura mata da sakon saki, ganin hakan yasa muka cigaba da yin rayuwarmu, naso ta amince min in aure ta saboda bani da burin daya wuce na mallake ta, nasan tana sona sai dai tafi ƙaunar takomama mijinta saboda ƴarta da tabar mashi" 


  Gaba ɗaya sun lura da canzawarshi, hakan Ya ƙara tabbatar masu da irin kaunar da yake yi mata.

  

Miƙewa yayi da sauri Ya nufi bedroom dinshi, Da sauri justice Yabi bayanshi, Yana Shiga Ya zura hannayenshi cikin aljihun short dinshi, Yayin da zuciyarshi ke cigaba da tafarfasa


  "Bana so hakan Ya dame ka, Yarinyar nan ko tana so ko bata so, Kai ne mijinta, Saboda kafi cutuwa, Tsawon shekara goma sha shidda kuna rayuwa agida ɗaya tamkar ma'aurata? Ka raineta ka kashe mata maƙudan kudi, Idan har ta butulce maka Allah ma bazai barta ba"


 Justice ne yayi maganar, yana daga tsaye abayanshi

  "Duk abunda nayi mata nayi ne don Allah..." kafin Ya ƙare maganar justice yace"nasan don Allah kayi mata amma wallahi bazan bari ta karya maka zuciya ba, tun da nake da kai baka ta6a nuna kana son wata ƴa mace ba, sai akanta, don haka dole ta aure ka, shi kuma mijinta Ya haƙura ya nemi wata, nasan ma yayi auranshi tun da jimawa"

 Juyawo Zaki yayi idanunsa akan justice Yace"nagode da kulawarka agare ni, amma mubar maganar, saboda hakan bamai yiwuwa bane, Ni bazan tursasa mata akan ta so ni ba, ta ɗauke ni tamkar yayanta tana girmamani, tun da nake da ita ban ta6a nuna mata inasonta da aure ba itama haka "

 "Ita ai ba makauniya bace, in ba kaiba wani namijine zai dauki dawainiyar baligar mace kamarta almost 16years, idan bazan manta ba, lokacin da naje gidanka a canada, ina lura da duk wani motsinku, Idan ka shiga daki da dare zaka kwanta tana binka bata fitowa har saita tabbatar da kayi bacci take fitowa, kaima kuma haka, sannan baka Iya cin abinci idan ba atare da ita ba, itama haka, kana nufin wani abu bai ta6a shiga tsakaninku ba"? ya faɗa yana bin sa da kallon tuhuma.


  "Nadeem, Ba abunda kake tunani bane, nasan nayi kuskure na ajiye macen da ba muharramata ba a gidana, amma wallahi ban ta6a shigarta ba..... " muryarshi na rawa ya ƙare maganar, wani irin yanayi yake jin kanshi tunawa da rayuwarshi da ita.

 

 Numfashi yaja kafin yaci gaba dacewa"Ta saba min da kanta, komai ita take yi min, bansan menene so ba sai akanta, ban fara muradin yin aure ba sai akanta, ashe ita din ba rabona bane...." 


  "Da ace kuɗi zasu Iya siyamin ita, wallahi har dukiyata zan iya salwantarwa saboda ita, bana tunanin zan samu macen da zata Iya maye min gurbinta, Ni ita kadai nakeso Nadeem" kwallar dake taruwa a cikin idanunsa har sun fara kokarin gangarowa saman kuncin sa.


Hankalin Justice Ba ƙaramin tashi yayi ba, ko a mafarki bai ta6a tunanin mace zata Iya tanƙwara zuciyar Zaki ba.


  Dafa kafadunsa yayi da hannayenshi

 "Inaso ka faɗamin shi mijinta tsawon shekara nawa su ka yi atare"?

 In a low voice zaki Ya furta"ƙasa da 2 years, ta faɗa min aranar data haifa mashi baby tabar gidan badan bata son shi ba, kawai taji ya futar mata arantane" 

  "Kasan mijin nata"?

"Taya za'ai nasan shi? ni ko sunan shi ban ruƙe ba, saboda kishinta da nake ji"

Murmushi justice yayi tare da ruko hannun Zaki, suka zaune gefen gadon shi.


  "Iyayenta masu hali ne"? ya jefa mashi tambayar.


"Yeah, mahaifinta ya ta6a ruke mukamin Governor a jihar joss, amma bai jima a mulkin ba ya sauka sakamakon ciwon kafar dake damun shi, bayan haka Ƙanin Mahaifinta Former president ne Na nigeria, Alhaji Musa wadata, Yayan Matar Uncle sharafudeen Hajiya Laurat, nima a wurin ta naji labarin ta" jinjina kai justice yayi"Ƴar masu Hali ce, Alhaji musan nan Yana ɗaya daga cikin wadanda suka fi kowa kuɗi a africa bayan family dinmu, amma nayi mamakin da har ta gudu tabar nigeria basu nemo ta ba, meyasa tabar mijinta da ƴarta? Shine abun tambayar"

   "Naikaina Labarinta Yajima Yana ɗaure min kaina, Sonta ne Ya makantar dani shiyasa ban mayar da ita ga Iyayenta ba, saima na taimaka mata wurin 6oye kanta agidana, naci gaba da bata kulawa"


   Justice ya ce Labarinta Akwai ruɗani Acikinsa, Ta fito daga babban family, ga ta kyakkyawa da ita amma ahaka har ta gudu daga gidan mijinta? Akan wani dalili? Me ta nema tarasa?"

      Ya faɗa yana kallon Zaki,

"Nayi kokarin nemanta don inji ya ta koma gidansu? Iyayenta sun kar6eta ko kuwa? Shine fargabana sai dai bani da hanyar da zan Iya kiranta, tabar min wayarta a hannuna, bansan kowa nata ba, in ba hajiya Laurat ba"

    Numfasawa Justice yayi kafin yace"kada ka damu ɗan uwana, zan iya yin komai akanka, gobe Idan Allah yakaimu a family dinner zanyi magana da hajiyar laurat din dangane da ita Yarinyar," har cikin ranshi yaji dadin maganar justice, ya kwantar mashi da hankalin shi sosai harya fara tunanin yadda haduwarsu zata kasance da ita, sun jima adakin suna tattaunawa daga bisani suka dawo falo wurin su Captain. 


______________________✍️



A hankali Motar Dr Jazz Ta ƙaraso bakin Entry Hall na shiga gidan baba Obie, Bayan yai parking ɗinta ya fito ya nufi cikin gidan, A katafaren Main Falo din gidan Ya taras da Twins zaune saman sofa tare da wani matashin saurayi kyakkyawan gaske kallo ɗaya zaka yima fuskarshi ka shaida ɗan uwan Justice ne, gaba ɗayan su wankan suit ne a jikin su, Cike da jin fargabansu Ya nufe su, Cikin sanyin murya yace"barkanku da hutawa"

 Ko kallo bai ishe su ba, Kamar Yayi magana da bango, kuma sun ganshi.

  Kusan sau uku Yana maimaita maganar da yayi masu amma babu wanda Ya amsa mashi, hakan Yasa shi yanke shawarar Tafiya yabar wurinsu Har Ya ɗaga ƙafa zai tafi muryar Zayn takatse shi.


 "Kai zo nan"! da kakkausar Murya Ya faɗa tare da yafuto shi da hannu, Irin kiran da akeyima kananin Yara, Jazz baiji komai aranshi ba Ya nufi Zayn.

 Yamutsa fuska zayn yai yayin da yake binshi da kaskantaccen kallo Yace

  "Kai makaho ne? Baka gan mu bane zaka wuce batare daka gaishe da mu ba"? Fuska adaure yayi mashi maganar.

   Cikin sanyin murya Jazz yace"Nayi maku magana kusan sau uku babu wanda Ya kula ni"

  Harara Zayn ya watsa mashi, Dr. nawaz dake a kishingide yana duban su Yace"zayn dama har yanzu wannan kwandon sharar Yana agidan nan? Nayi tsammanin Uncle Mubarak Ya saki babarsa sun koma kasarsu"

  Ta6e baki Zayn yayi"gayanan dai kana kallon shi, baida banbanci da masu gida, Har yafi mu jin daɗi, Uncle Mubarak ya ɗaure mashi wurin zama" 

  Yamutsa fuska Dr.Nawaz Yai"Kaci sa'a ba'a ƙasar nake zaune ba, da tuni nasa anyi watsi dakai, donni bana son bare ya ra6i Ahlinmu," Jazz dake atsaye yana sauraron Rashin mutuncin da suke yi mashi, tuni idanunsa sun cicciko tab da kwalla.

 "Ya isa haka!" Zaid ne Ya faɗa tare da kallon Jazz, Da hannu Yayi mashi alamar Ya tafi, bawan Allah Jiki asanyaye ya nufi Hanyar kitchen din gidan, tunkafin Ya karasa Able ta fito daga ciki hannunta ruƙe da tray na kayan marmari, ganin jazz yasa ta dakata da tafiya fuskarta da fara'a tace"Jazz Ya jikin naka"?

 Fuskar shi babu walwala Yace"da sauki"

 "Allah Ya kara lafiya" ya amsa mata da ameen, ganin Yana ƴan kalle kalle Ne yasa ta fahinci akwai wani abu da yake nema don haka tace"ko akwai wani abu da kake bukata ne"?

   Ɗaga mata kai Yai haɗi da cewa"Eh, Ina neman Faryat ne,"

  "Muje na raka ka, Nima wurin su zanje kai masu Kayan marmari," amsa mata yayi da toh, ta yi gaba yabi bayanta, aranta ta ayyana ko me zai kai shi wurin faryat? Tantiriyar Yarinyar nan da babu Allah aranta"

 Upstairs suka hau, bayan sun sauka third floor, suka nufi Balcony dake acan sama,Tsayawa fasalta kyawun wurin 6ata baki ne sai wanda Ya gani, tunkafin su karasa Jazz Ya hango Su zazzaune saman wasu hadaddun Kujeru Bugun Dubai, Matasan Ƴan mata ne masu ji da kansu, A kalla sun kai su uku Kowaccensu Ta dauki wanka na kece raini, Kamshin turarensu tuni Ya soma Cika mashi hancinshi.


     Kaitsaye idanunsa suka sauka akan Faryat, wadda ke asanye da mini skirt ya matse jikinta, daƙyar skirt din Ya wuce Ass dinta, Rigar jikinta kuwa Ko cibinta bata rufe ba, ta bayyana shape din kirjinta hatta nipples dinta kana iya ganin tsininsu, babu mayafi akanta Kitson kalabar da akayi mata ne mai kyan gaske ansanya mata sparkling stones masu jan hankali saman gashin kanta, yatsun hannunta yana asanye da gold knuckle rings, Haka zalika Hancinta na amanne da nose ring, wata ziririyar sarka ce a kafarta, Yarinyar karshe ce wurin Iya barikanci, Hatsabibiyar gaske bata jin magana ko miskala zarratin, sai dai fa akwai kyan sura, komai nata irin na hajiya saratu ne banbancinsu girman jiki da shekaru.


  Matashiyar dake a gefenta, Yusra ce Ƙanwar Yaseer, Kallo ɗaya zakai mata saika sake kallonta, Tsabar haɗuwarta, itama fara ce sol, kamanninta sak dana mahaifiyarta Her excellency Muhibbat, gata doguwa tubarkalla, bayan ita sai Zulaihat kanwar Ziyad Wankan tarwaɗa ce alaunin fata tana da saukin kai ko a fuska ka kalle ta, babu wanda Ya lura da Jazz A cikinsu Hankalinsu na akan firar da suke Yi.


  able ce tayi masu sallama, Tare da ajiye masu tray din kayan marmarin saman round table din dake a tsakiyar kujerun su, juyawa tayi da sauri ta fuce tabar wurin.

   Wani irin shakkar Yi masu magana Yake ji, Sai faman bin Faryat Yake Yi da kallon ƙurulla.


  "Na jaraba kiran layin Sister Hindu bata yi picking ba, may be ko bata a kusa ne da wayar, ita dai Yazrin nayi mata uziri, saboda tafiyar da suka sha nasan haryanzu gajiyar tafiya bata sakesu ba" Zalaihat ce tayi maganar tare dakai hannu ta dauki tufa tana ci

  "Ina ga mezai hana mu shiga gidan yi masu bangajiyar tafiya, Su mommy ma suna acan"

   "Ni dai ba inda zanje, sai zuwa gobe idan mun haɗu wurin Dinner din daddy Hateem" Acewar Faryat Tana faɗa tana farfari da idanunta.

  "Gobe akwai shagali, zamu yi sharholiyarmu son ran mu, Har nakagara goben nan tayi," Yusra ce ta fada tana karkaɗa kafarta.

     Har Faryat Ta buɗe baki daniyar tayi magana, Sautin ringing din wayar Jazz Ya dakatar da ita, Kusan atare suka wurga idanunsu kan fuskarshi, nan take yaji gabanshi ya faɗi rass saboda kwarjinin da suka yi mashi.


     Yamutsa fuska Yusra tayi tare da kau da idonta 

 Zulaihat kuwa Murmushi tasakar mashi

  "Dan uwa, Tun yaushe kazo wurin nan ne? 

  Yana faman Kame kansa Yace"tare da abla muka zo"

  "Amma meyasa bakayi mana magana ba jazz," cikin kulawa ta fada tana dubanshi  Ta fuskanci Hankalin shi ba kwance yake ba

  "Wa kake nema ne"?

 Kallon Faryat da yayi ne yasa ta gane ita yake son gani"

 Murmushi zulaihat tayi,

Faryat dake kallon shi, wani irin shu'umin murmushine akan fuskarta, yunƙurawa tayi ta miƙewa ta dubi su Yusra"ni zan shiga ciki, bazan jima ba yanzu zan dawo" Yusra dake harararsa tace"faryat kin bani kunya, Ki rasa wa zaki kula sai wannan halittar" ta fada tana nuna shi da yatsa

 Zulaihat tace"Please Yusra, babu ruwanki da shiga sabgarsu" Ta6ebaki Yusra tayi

  Ba tare daya ankare ba, Faryat ta ruƙo hannunsa tare da jan shi suka soma tafiya atare, wani sanyine yaji ya ratsa zuciyarsa, duk da yasan ba lallai Faryat ta sassauta mashi ba, Ya riga daya san halin ta.

 Kaitsaye suka nufi bedroom dinta dake a gidan, adai dai bakin kofar shiga Dr.Jazz Ya dakata da tafiya, da sauri ta kalle shi hadi da kashe mashi ido ɗaya tace "my babe meyasa ka dakata da yin tafiya? Let's go inside," ta fada tana matse hannunsa dake acikin nata, har cikin zuciyarshi yake jin matsar da take yi mashi. Muryarshi ƙasa ƙasa Ya ce"basai na shiga ciki ba, mu koma falo mu yi magana" 

Ɗaure mashi fuska tay "Jazz, you will lose your chance to talk to me if you don't go in," she warned. "If you don't go in, don't expect to see me again"!

*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*

 *Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*

3196407426

First bank 

Bature Hafsat Muhammad,

 *bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*

Post a Comment

Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post Next Post

Sponsored Link

Sponsored Post